Labarai
Gwamnan Jihar Nasarawa Ya Rusa Majalisar Zartaswar Jihar
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya rusa majalisar zartaswar jihar nan take.
Gwamnan ya kuma sallami sakataren gwamnatin jihar Barista Mohammed Uban Doma Aliyu daga mukaminsa.
Ya sanar da hakan ne yayin taron majalisar zartarwar na gaggawa da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Lafiya, babban birnin jihar.
Ya umurci dukkan kwamishinonin da su mika al’amuran ma’aikatunsu ga manyan sakatarori, yayin da shi ma sakataren gwamnatin zai mika nasa ayyukan su ga babban sakatare mai kula da harkokin majalisar zartaswar jihar.
Gwamna Abdullahi Sule ya yabawa ‘yan majalisar zartaswar da sakataren gwamnatin jihar, bisa yadda suka yi aiki a gwamnatinsa.
Ya kuma bayyana jajircewarsu wajen gudanar da ayyukansu a matsayin abin yabawa, inda ya yi fatan samun nasara a ayyukansu na gaba.
A jawabin da ya yi a madadin sauran kwamishinonin, kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar Barista Labaran Shu’aibu Magaji, ya godewa gwamnan bisa damar da aka basu na yin aiki a gwamnatinsa.
Daga Aliyu Muraki
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
