Connect with us

Kasuwanci

Gwamna Yusuf Ya Gwangwaje Kano Pillars Da Sabbin Motocii

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ta bai wa ƙungiyar kwallon ƙafa ta Kano Pillars Football Club sabbin motoci uku domin sauƙaƙa musu matsalolin sufuri a yayin gasar Premier ta shekarar 2025/2026 da ke gudana.

 

Motocin sun haɗa da babbar motar Marcopolo mai kujeru 29 don ɗaukar ’yan wasa, motar samfurin Hummer, da kuma Sharon da za a yi amfani da ita wajen harkokin gudanarwa da sufuri.

 

A lokacin da yake mika makullai da takardun motocin a madadin Gwamnan, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Malam Ibrahim Umar Farouk, ya roƙi matasan jihar masu son wasanni da su ci gaba da zama masu bin doka da oda tare da guje wa duk wani abu da zai bata sunan jihar.

 

Ya bayyana cewa wannan kyauta ta nuna yadda Gwamna Yusuf ke da ƙwarin gwiwa wajen ƙarfafa matasa da bunƙasa harkokin wasanni a jihar.

 

A nasa jawabin, Kwamishinan Matasa da Wasanni, Mustapha Kwankwaso, ya bayyana godiyarsa ga Gwamna Yusuf bisa wannan babban ci gaba da zai ƙara wa ’yan wasan kwarin gwiwa da jin daɗin aiki.

 

Ya kuma yi kira ga magoya bayan ƙungiyar Sai Masu Gida da su kasance masu ladabi da biyayya tare da ci gaba da nuna goyon baya cikin lumana.

 

Da yake mayar da martani, Manajan Janar na Kano Pillars FC kuma kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa (MON, OON), ya yaba wa Gwamna Yusuf bisa goyon baya da ƙaunar da yake nuna wa ƙungiyar.

 

Ahmed Musa ya kuma roƙi gwamnatin jihar da ta ba da girmamawa ta musamman ga tsohon kyaftin ɗin ƙungiyar, Rabiu Ali, domin tunawa da gudunmawar da ya bayar wajen bunƙasa kwallon ƙafa a Najeriya, yana mai kiran sa da “ɗaya daga cikin fitattun ’yan wasa mafiya tasiri da suka taka leda a tarihin NPFL.”

 

A halin yanzu, ƙungiyar Kano Pillars za ta karɓi bakuncin Niger Tornadoes ta Minna a wasansu na ranar goma ta gasar NPFL a wannan Asabar, a filin wasa da suka ɗauka a matsayin gida na wucin gadi — Filin Muhammadu Dikko da ke Katsina.

 

Khadijah Aliyu

 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara