Labarai
Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da bayar da tallafin kuɗi ga ma’aikatan gwamnati da na gidan gwamnati su 3,682 a jihar.
Ya bayyana cewa wannan shiri wani ɓangare ne na tsarin kula da jin daɗin ma’aikatan gwamnatinsa, wanda ke da nufin tallafa wa ma’aikata da sauran marasa ƙarfi, musamman a cikin watan Ramadan.
A cewarsa, kayan tallafin da suka haɗa da shinkafa, da taliya da sauran muhimman kayan abinci, an samar da su ne domin bai wa ma’aikata da iyalansu damar gudanar da azumi cikin sauƙi da walwala.

Ya ƙara da cewa wannan tallafi ya zo ne a matsayin kari ga sauran shirye-shiryen tallafin Ramadan da ake aiwatarwa a faɗin jihar.
Hakan ya haɗa da babban shirin ciyarwa da ake gudanarwa a kusan cibiyoyi 640 da ke cikin gundumomin siyasa 287.
Bayan samar da abinci, Gwamna Namadi ya ce shirin na kuma taimakawa tattalin arzikin cikin gida, ta hanyar samar da ayyukan wucin gadi ga kusan mutane 6,000, ciki har da masu girki da masu kula da rabon kayan abinci.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnati ta faɗaɗa shirin domin ya haɗa da makarantun Tsangaya, inda makarantu 562 a cikin ƙananan hukumomi 27 ke cin gajiyar shirin a wannan watan Ramadan.
Da yake bayyana watan mai alfarma a matsayin lokaci na tausayi, sadaukarwa da kyautatawa, Gwamnan ya jaddada alhakin gwamnatinsa na ƙarfafa haɗin kai ta hanyar shirye-shiryen jin ƙai da aka tsara yadda ya dace.
Ya kuma ce rabon kayan abinci ga ma’aikata na nuna yadda gwamnatinsa ke girmama gudummawar da suke bayarwa wajen bunƙasa jihar. Yana mai cewa za a bai wa kowane daga cikin wadanda suka amfana da tallafin kuɗi naira 20,000, inda jimillar kuɗin da za a raba ta haura naira miliyan 12.

Don haka, Malam Umar Namadi ya yi kira ga al’umma da su yi aiki da koyarwar addinin Musulunci ta hanyar taimakon juna tare da yin addu’o’i domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Jigawa da Najeriya baki ɗaya.
A nasa jawabin, Kwamishinan Ma’aikatar Jin Kai, Alhaji Auwalu Sankara, ya yaba wa gwamnan bisa faɗaɗa shirye-shiryen tallafin Ramadan a jihar.
Ya ce adadin waɗanda ke amfana da shirin ciyarwar Ramadan ya ƙaru sosai a ƙarƙashin wannan gwamnati, inda ya tashi daga kusan mutane miliyan shida zuwa sama da miliyan takwas.

Ya ce ci gaba da faɗaɗa shirin a kowace shekara na nuna ƙudirin gwamnati na tabbatar da cewa babu wanda zai shiga watan Ramadan cikin yunwa.
Ma’aikatar Jin Kai da Agajin Gaggawa ce ke kula da rabon tallafin tare da haɗin gwiwar Ofishin Shugaban Ma’aikatan Jiha domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.
Wasu daga cikin waɗanda suka amfana sun nuna godiyarsu ga Gwamna Namadi, inda suka bayyana tallafin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci, la’akari da tsadar rayuwa da ake fuskanta a halin yanzu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
