Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Bada Goron Sallah Ga Alhazan Jihar Jigawa

Published

on

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya bada Riyal 100  a matsayin goron Sallah ga  mahajjata jihar su  1,298.

Amirul Hajj na jihar kuma mai martaba Sarkin Hadejia Dr. Adamu Abubakar Make ya bayyana haka a lokacin da ya ziyarci masaukin Alhazai a Makkah.

Sarkin ya bayyana cewa, an dauki matakin ne don rage wahalhalun da Alhazai suka fuskanta a sakamakon dala 400 da aka ba su ta kudin guzuri saboda matsalar tashin Dala.

Ya yi kira ga maniyyatan da su yi addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

 

Dakta Adamu Abubakar Maje ya kuma yabawa dan jaridan nan na tawagar manema labarai ta jihar, Alhaji Abba Sa’idu Limawa wanda ya tsinci kudaden kasashen waje a Madina kuma ya mayar da ga  hukumar Alhazai ta kasa NAHCON,  ta hannun hukumar alhazai ta jihar Jigawa.

Shi ma da yake nasa jawabin babban daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yabawa mahajjatan bisa bin ka’idojin da aka gindaya na masarautar Saudiyya.

Ya yi kira ga maniyyatan da kada su wuce nauyin kilogiram  8 a jakar su ta   hannu da kuma kilogiram 32 a babbar jaka.

Wasu daga cikin Alhazan da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun godewa Gwamna Namadi bisa wannan karamci da aka yi musu, sannan sun yi alkawarin ci gaba da zama jakadu nagari ga jihar yayin da suke kasa mai tsarki.

A baya dai Gwamna Namadi ya biya Naira miliyan daya ga kowane maniyyacin aikin Hajjin 2024.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa,  tawagar gwamnatin da ta raka Amirul Hajj ya hada da mataimakin kakakin majalisar jiha, shugaban kwamitin majalisar kan aikin hajji da dai sauransu.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara