Labarai
Gwamna Namadi Ya Bada Goron Sallah Ga Alhazan Jihar Jigawa
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya bada Riyal 100 a matsayin goron Sallah ga mahajjata jihar su 1,298.
Amirul Hajj na jihar kuma mai martaba Sarkin Hadejia Dr. Adamu Abubakar Make ya bayyana haka a lokacin da ya ziyarci masaukin Alhazai a Makkah.

Sarkin ya bayyana cewa, an dauki matakin ne don rage wahalhalun da Alhazai suka fuskanta a sakamakon dala 400 da aka ba su ta kudin guzuri saboda matsalar tashin Dala.
Ya yi kira ga maniyyatan da su yi addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

Dakta Adamu Abubakar Maje ya kuma yabawa dan jaridan nan na tawagar manema labarai ta jihar, Alhaji Abba Sa’idu Limawa wanda ya tsinci kudaden kasashen waje a Madina kuma ya mayar da ga hukumar Alhazai ta kasa NAHCON, ta hannun hukumar alhazai ta jihar Jigawa.
Shi ma da yake nasa jawabin babban daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yabawa mahajjatan bisa bin ka’idojin da aka gindaya na masarautar Saudiyya.

Ya yi kira ga maniyyatan da kada su wuce nauyin kilogiram 8 a jakar su ta hannu da kuma kilogiram 32 a babbar jaka.
Wasu daga cikin Alhazan da suka zanta da gidan rediyon Najeriya sun godewa Gwamna Namadi bisa wannan karamci da aka yi musu, sannan sun yi alkawarin ci gaba da zama jakadu nagari ga jihar yayin da suke kasa mai tsarki.

A baya dai Gwamna Namadi ya biya Naira miliyan daya ga kowane maniyyacin aikin Hajjin 2024.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tawagar gwamnatin da ta raka Amirul Hajj ya hada da mataimakin kakakin majalisar jiha, shugaban kwamitin majalisar kan aikin hajji da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
