Fasaha
FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
Gwamnatin tarayya ta ce tace a shirin ta sauya wuraren dake bushe a sassan arewacin Nijeriyaza a raba naira miliyan miliyan 3.4 kuma akasarin wadanda zasu amfana da wannan za su kasance mata ta hanyar Shirin ACReSAL.
Da yake jawabi a wajen bude taron kwanaki 10 na masu ruwa da tsaki kan tsarin kula da tsare-tsare (SCMP) na sabbin magudanan ruwa guda 11 a fadin Jihohi bakwai na tarayya a Ilorin, kodinetan ayyukan ACRESAL na kasa, Mista Abdulhamid Umar, ya ce za a gudanar da aikin ne ta hanyar shirin kawo sauyi na dogon lokaci.
Jami’in kula da ayyukan na kasa na ACRESAL Adamu Shettima wanda ya samu wakilcin kwararre a bangaren kula da ayyukan ruwa na gwamnatin tarayya, Adamu Shettima, ya bayyana cewa aikin yana da nasaba da dawo da martabar yankuna da suke bushe, daidaita yanayin muhalli da kuma karfafa miliyoyin al’umma a fadin Arewacin Najeriya.
Umar ya bayyana cewa bankin duniya ne ke taimaka wa aikin ta hannun kungiyar ci gaban kasa da kasa (IDA), ya kara da cewa wannan shi ne karon farko da gwamnatin tarayya ke samar da tsarin kula da ruwa mai girman irin wannan.
Ya yi nuni da cewa, dabarun da masu ruwa da tsaki za su mayar da hankali wajen yin mu’amala da masu ruwa da tsaki a dabarun da suka shafi Kwara, mai masaukin baki, Kaduna, Kebbi, Zamfara, Niger da FCT.
A nata jawabin, kwamishiniyar muhalli ta jihar Kwara, Hajia Nafisat Musa Buge, ta bayyana cewa hadakar masu ruwa da tsaki na daga cikin shirin inganta sha’anin ruwa, da inganta yanayin da ake ciki, da inganta rayuwa mai ɗorewa a yankunan da ke fama da wannan matsala a Najeriya.
Kwamishinan, ta ce sabon Shirin zai kasance ne tsakanin jihohi shida na Najeriya.
A nasa jawabin, Ko’odinetan shirin ACRESAL na jihar Kwara, Alhaji Shamsideen Aregbe, ya bukaci a hada kai da masu ruwa da tsaki wajen samar da tsare-tsare na kula da ruwan.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
