Connect with us

Labarai

Gwamna AbdulRazaq, Saraki da Sarkin Ilorin Sun Taya Musulmi Murnar Sallah

Published

on

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, tare da Sanata Abubakar Bukola Saraki da Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, sun taya al’ummar Musulmi murnar bikin Eid-el-Fitr, wanda ke nuna ƙarshen azumin watan Ramadan.

A cikin wata sanarwa, Gwamna AbdulRazaq ya roƙi Allah da Ya karɓi ibadun da aka yi da addu’o’in da aka gabatar a tsawon watan Ramadan, tare da roƙonSa da Ya ba wa bayinsa ikon ci gaba da kasancewa masu biyayya da ƙasƙantar da kai gare Shi.

Haka kuma ya buƙaci Musulmi da su ci gaba da riko da kyawawan halaye da watan Ramadan ya koyar, tare da kiyaye umarnin Allah a kowane lokaci.

Shi ma tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dakta Abubakar Bukola Saraki, a cikin wata sanarwa da jami’in sa kan harkokin cikin gida, Abdulganiyu Abdulqadir ya fitar, ya taya Musulmi a Najeriya da sauran sassan duniya murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara.

Ya kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su ci gaba da kasancewa masu fata da haɗin kai duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

A nasa ɓangaren, Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, cikin saƙon da mai magana da yawunsa, Abdulazeez Arowona ya fitar, ya taya daukacin al’ummar Musulmi a Daular Ilorin da Jihar Kwara da ma ƙasar Najeriya baki ɗaya murnar kammala azumin watan Ramadan na shekarar 1447 Hijira (2026 Miladiyya).

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara