Ilimi
Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a matsayin ginshiƙin ci gaban kasa.
Ya bayyana hakan ne lokacin da ya jagoranci wata tawaga domin zagayawa makarantun yankin, don duba yadda ake koyarwa da kuma hanyoyin ilmantarwa.

A cewarsa, ziyarar na daga cikin ƙoƙarinsa na inganta tsarin ilimi a ƙaramar hukumar Birnin Kudu, wanda ya yi daidai da kudurori 12 na Gwamna Umar Namadi.
Muhammad Uba ya kuma duba wasu makarantu daban-daban, inda ya tattauna da malamai da ɗalibai domin tantance ci gaba da kuma gano wuraren da ke buƙatar gyara.

Wannan ziyara ta biyo bayan wasu sabbin ci gaba a ɓangaren ilimi na ƙaramar hukumar, ciki har da bayar da sabuwar mota ga Hukumar Ilimi ta Ƙaramar Hukuma daga Gwamnatin Jihar Jigawa ta hannun Ma’aikatar Ilimin Firamare.
Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma tabbatar da an saka sabbin tayoyi a motar, wanda ke nuna jajircewarsa wajen tallafa wa ilimi a yankin.

A nasa jawabin, shugaban hukumar Ilimin Bai Daya na jihar (SUBEB), Haruna Idris Hadejia, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa ƙoƙarinsa da jajircewarsa wajen bunƙasa ilimi a Birnin Kudu.
Ya bayyana Dakta Builder Muhammad a matsayin jajirtacce da ya yi fice a Jihar Jigawa, inda ya nuna yadda yake da himma wajen aiwatar da ayyukan ci gaban ilimi.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai7 days agoKebbi: An Samu Asarar Rayuka a Rikicin Alwasa
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
