Connect with us

Ilimi

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a matsayin ginshiƙin ci gaban kasa.

Ya bayyana hakan ne lokacin da ya jagoranci wata tawaga domin zagayawa makarantun yankin, don duba yadda ake koyarwa da kuma hanyoyin ilmantarwa.

A cewarsa, ziyarar na daga cikin ƙoƙarinsa na inganta tsarin ilimi a ƙaramar hukumar Birnin Kudu, wanda ya yi daidai da kudurori 12 na Gwamna Umar Namadi.

Muhammad Uba ya kuma duba wasu makarantu daban-daban, inda ya tattauna da malamai da ɗalibai domin tantance ci gaba da kuma gano wuraren da ke buƙatar gyara.

Wannan ziyara ta biyo bayan wasu sabbin ci gaba a ɓangaren ilimi na ƙaramar hukumar, ciki har da bayar da sabuwar mota ga Hukumar Ilimi ta Ƙaramar Hukuma daga Gwamnatin Jihar Jigawa ta hannun Ma’aikatar Ilimin Firamare.

Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma tabbatar da an saka sabbin tayoyi a motar, wanda ke nuna jajircewarsa wajen tallafa wa ilimi a yankin.

A nasa jawabin, shugaban hukumar Ilimin Bai Daya na jihar (SUBEB), Haruna Idris Hadejia, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa ƙoƙarinsa da jajircewarsa wajen bunƙasa ilimi a Birnin Kudu.

Ya bayyana Dakta Builder Muhammad a matsayin jajirtacce da ya yi fice a Jihar Jigawa, inda ya nuna yadda yake da himma wajen aiwatar da ayyukan ci gaban ilimi.

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara