Connect with us

Labarai

Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu

Published

on

Firaminista Mark Carney ya ce Canada ta shirya amincewa da kafa ƙasar Falasɗinu a cikin watan Satumba, inda ta zamo ƙasa ta uku daga cikin ƙungiyar G7 da ta fitar da irin wannan sanarwa a cikin kwanakin nan.

Carney ya ce za su ɗauki matakin ne ta la’akari da wasu sharuɗɗan gyara daga ɓangaren hukumomin Falasɗinu da suka haɗa da amincewa da tsarin dimokuraɗiyya da kuma gudanar da zaɓe ba tare da ƙungiyar Hamas ba a shekara mai zuwa.

Sanarwar tasa na zuwa ne kwana ɗaya bayan Birtaniya ta bayyana goyon bayan ta ga kafa ƙasar Falasɗinun a watan Satumba mai zuwa, kuma mako ɗaya bayan Faransa ta yi irin wannan sanarwa.

Ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila ta yi watsi da sanarwar ta Canada tana mai cewa matakin tamkar jinjinawa ƙungiyar Hamas ne.

Daga cikin ƙasashe 193 na Majalisar Dinkin Duniya, 147 sun goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu.

Amma Mr Carney ya ce Canada za ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinun ne a babban taron Majalisar Dinkin Duniya mai zuwa.

Ya kafa hujja da yadda Isra’ila ke ƙara mamaye sassan gaɓar yamma da kogin Jordan da taɓarɓarewar ayyukan jin ƙai a Gaza da kuma harin da Hamas ta kai wa Isra’ila a ranar bakwai ga watan Oktoba a matsayin dalilan da suka sa Canada ta sauya matsayarta a kan batun.

Carney ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba cewa “Mawuyacin halin da ake ciki a Gaza na ƙara taɓarɓarewa,”

Ya ce kafa ƙasar Falasɗinu zai bai wa jagororin Falasɗinawa damar gudanar da tsare-tsaren mulki da gudanar da zaɓuka ba tare da Hamas ba a 2026 da kuma kawo ƙarshen ayyukan ƙungiyoyi masu riƙe da makamai a yankin.

Dama can Canada ta daɗe tana goyon bayan shirin kafa ƙasashe biyu masu ƴancin kansu a matsayin hanyar warware rikicin Falasɗinawa da Isra’ila.

Carney ya kuma ce ya tattauna da shugaban Falasɗinawa Mahmud Abbas a kan batun.

Hukumomin Falaɗinawa dai suna iko da wasu sassa na gaɓar yamma da kogin Jordan a ƙarƙashin jam’iyyar Fatah da shugaba Abbas ke jagoranta, yayin da ƙungiyar Hamas ke tafiyar da Gaza. Dukkan su ba su taɓa gudanar da zaɓe ba tun a 2006.

Firaminitan Canada ya fuskanci matsin lambar neman ya sanar da matsayar sa kan kafa ƙasar Falasɗinu tun bayan da manyan ƙawayen ƙasarsa, Birtaniya da Faransa suka sanar da goyon bayan su.

Jakadun Canada da jami’an diflomasiyyarta fiye da 200 suka sanya hannu kan wata takarda mai neman Carney ya amince da shirin

A cikin wasiƙar da suka aikewa Carney jami’an sun ce yaƙin da Isra’ila ke yi a Gaza ya yi hannun riga da tsarin ƙasar.

Da aka tambaye shi ko Canada ta goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinun ne saboda Birtaniya ta janye hankalin ta, sai Mr Carney ya ce ƙasarsa ta ɗauki matakin ne ba tare da katsalandan daga wata ƙasa ba.

Carney ya jaddada cewa Canada ƙasa ce mai ƴancin kanta kuma wadda ke da ikon tsara yadda za ta yi alaƙa da ƙasashen duniya.

Da wannan mataki dai ana iya cewa Canada ta bi turbar da sauran ƙawayenta na Turai suka bi game da kafa ƙasar Falasɗinu.

Idan Birtaniya da Faransa suka jaddada goyon bayansu ga kafuwar ƙasar Falasɗinu, zai rage saura Amiurka ce kaɗai ke adawa da hakan a cikin ƙasashe mambobin dindindin a kwamitin taro na Majalisar Dinkin Duniya.

Ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce mutane aƙalla 60,034 aka kashe a Gaza tun bayan fara yaƙi a Gaza, kuma ta ce aƙalla 1,200 daga cikin su sun mutu ne saboda rashin abinci mai gina jiki, yayin da 89 a cikin su ƙananan yara ne.

BBC/Hausa

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara