Ilimi
Daliban Jami’ar Nasarawa 3 Sun Mutu A Tirmitsitsin Rabon Tallafi
Daliban Jami’ar Jihar Nasarawa 3 ne ake fargabar sun mutu sakamakon turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafin shinkafa da gwamnatin jihar ta bada a yau Juma’a a garin Keffi.
Lamarin ya faru ne a dandalin taro na makarantar inda aka ajiye buhunan shinkafa ana jiran isowar gwamna Abdullahi Sule domin fara rabon kayayyakin.
A cewar wani dalibin da lamarin ya faru a gaban idonsa, Moses Ajah, ya ce gungun daliban da ke dakon shiga dandalin sun ci karfin jami’an tsaro tare kutsawa dandalin taron.
Ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici matuka.
Ya ce wasu dalibai sun kwashi buhunan shinkafan suka gudu da su duk da cewa Gwamnan bai kai ga iiowa wurin ba domin kaddamar da rabon.
Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, an ga jami’an ‘yan sanda suna bin daliban dakunan kwanansu don kwato buhunan shinkafar da suka yi awan gaba da su.
Da aka tuntubi jami’in yada labarai da kula da jami’ar, Mista Abraham Ekpo, ya ce yana sane da lamarin amma har yanzu bai samu cikakken bayani a kai ba.
Aliyu Muraki
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
