Ilimi
Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
Daga Usman Muhammad Zaria
Daliban makarantu daga jihohin Arewa maso Yamma da suka hada da Kano, Jigawa da Katsina sun yi kira ga masu ruwa da tsaki da su samar musu da tsaro, ingantaccen kiwon lafiya, da taftataccen ruwan sha.
Daliban sun yi wannan kiran ne yayin bikin Ranar Yara ta Duniya da aka gudanar a Kano, wanda Hukumar Kula da Yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ta shirya.
Haka zalika ɗaliban sun nemi a mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta domin samun ilimi mai inganci.

Haka kuma, sun buƙaci a aiwatar da dokokin kare haƙƙin yara tare da ba da dama ga daidaito tsakanin jinsi, musamman a fannin ilimin ’ya’ya mata.
Bugu da ƙari, sun koka kan wariyar jinsi, rashin kula da lafiyar ’ya’ya mata yayin al’ada, tare da neman adalci game da cin zarafin yara.
Har ila yau, sun nemi haɗin kai domin inganta walwalar yara a Najeriya a duk matakai.

Yaran sun sake neman goyon bayan kafofin watsa labarai domin yaɗa bukatunsu da kuma tabbatar da samun haƙƙoƙinsu.
A jawabinsa yayin taron, Shugaban Ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Mohammed Farah, ya bayyana cewa UNICEF tana ba da tallafi ga gwamnati wajen magance kalubalen da suka shafi yara.
Ya jaddada cewa domin tabbatar da kowane yaro a Najeriya ya rayu, ya sami ilimi, ya girma cikin mutunci da tsaro, UNICEF na kira ga haɗin gwiwar duk masu ruwa da tsaki domin canja yanayin.

Farah ya tabbatar da kudirin UNICEF na ci gaba da aiki tare da gwamnati, al’umma da ƙungiyoyin farar hula, domin tabbatar da cewa kowane yaro a Najeriya na iya rayuwa, samun ilimi da bunƙasa.
Ya bayyana cewa, tabbas Najeriya ta samu ci gaba, amma akwai buƙatar gaggawa, haɗin kai da ɗorewar aiki domin kare makomar yara.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
