Connect with us

Ilimi

CORET Zata Ciyarda Makarantun Makiyaya Shida A Jihohin Kaduna Da Jigawa

Published

on

 

Kungiyar Tarayyar Makiyaya ta CORET ta ce zata tallafawa yara makiyaya 1,600 a makarantun makiyaya guda shida a Jihohin Kaduna da Jigawa a wani yunƙuri na rage ƙarancin abinci da rashin ingantaccen abinci.

 

Sakataren Janar na CORET, Mohammed Bello Tukur ne ya bayyana hakan a lokacin ƙaddamar da shirin ciyar da ɗalibai na haɗin gwiwa a Laddauga, wurin kiwon dabbobi na Kachia a Jihar Kaduna.

 

Ya bayyana cewa, manufar wannan shiri ita ce tallafa wa shirin ciyar da ɗalibai na makarantun makiyaya.

 

Sakatare Janar ya ƙara da cewa kashi 60 na waɗanda za su amfana ‘yan mata ne, kuma shirin zai ƙarfafa ilimin kyawawan ɗabi’u a fannin abinci mai gina jiki, tsafta, tsabtace muhalli, da kuma sarrafa albarkatun ƙasa yadda ya dace.

 

Mohammed Bello Tukur ya bayyana cewa shirin yana kuma da niyyar samar da damammakin tattalin arziki da haɗin kai ga mata a cikin al’ummomin makiyaya guda shida da aka zaɓa.

 

“Muna son rage nauyin ciyar da ɗalibai da ke kan iyaye da kuma ƙara yawan yara da ke shiga makaranta. Bayan Kaduna, muna kuma duba Jihar Jigawa, Katsina, Taraba, Adamawa da Neja. Mun haɗa al’umma don dorewar shirin. Muna son gudanar da shirin na tsawon watanni 36.”

 

A jawabin Ministan Raya Dabbobi, ya bayyana cewa wannan shiri ya zo a daidai lokaci, kuma zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira.

 

“Shirin zai samar da abinci mai gina jiki ga yara wanda zai ƙara musu basira kuma zai ƙarfafa su wajen zuwa makaranta, wanda hakan zai rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta. Haka kuma zai sa su zama masu amfani ga al’umma.”

 

Ministan wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa na Musamman, Dr. Ishaq Bello, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bullo da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta kiwon dabbobi a ƙasar.

 

Tun da farko, Daraktan Noma da Raya Kauyuka na ECOWAS, Alain Traore wanda Dr. Saater Kumaga ya wakilta ya bayyana cewa ECOWAS na aiwatar da ayyuka 127 a ƙasashe memba 15.

 

Ya bayyana cewa daga cikin waɗannan ayyuka, guda uku ana aiwatar da su ne a Jihar Kaduna.

 

Manajan shirin, Dr. Abdullahi Umar ya gode wa al’ummar Kachia, yana mai roƙon su su bayar da haɗin kai don nasarar shirin.

 

Hakimin Ladduga, Alhaji Ahmed Jibril ya tabbatar wa CORET da cikakken haɗin kai don nasarar shirin.

 

An aiwatar da shirin ne a Kachia, wurin kiwon dabbobi na Laddauga a Jihar Kaduna da kuma Maigatari Trans-boarder axis a Maigatari LGA Jihar Jigawa, tare da tallafin Hukumar ECOWAS – Cibiyar Raya Yankin Noma (RAAF) da haɗin gwiwar Kungiyar Taimakon Ci Gaba ta Sifen (SDC).

 

Makarantun da aka zaɓa a Kaduna sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Wuro Nyako wurin kiwon dabbobi na Kachia, Makarantar Firamare ta Makiyaya Mbela Biradam Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia, da Makarantar Firamare ta Makiyaya Tiggirde Ladduga wurin kiwon dabbobi na Kachia.

 

A Maigatari Trans-boarder axis a Jigawa kuwa sun haɗa da: Makarantar Firamare ta Makiyaya Lawan Dutsi, Makarantar Firamare ta Makiyaya Bulama Kauje da Makarantar Firamare ta Makiyaya Gidan Tinau.

 

COV: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara