Connect with us

Labarai

CAN Ta Yaba Saboda Agajin Gaggawa Ga Mutanen Da Fashewar Tanka Ta Shafa a Neja

Published

on

Kungiyar kiristocin Najeriya reshen jihar Neja (CCN) ta yaba da martanin gaggawar da gwamna Umar Mohamed Bago ya yi kan fashewar tankar da ta afku a mahadar Diko da ke karamar hukumar Gurara a jihar.

 

Shugaban karamar hukumar Daniel Tsado wanda ya yi wannan yabon a cikin wata sanarwa da ya fitar a Minna, ya ce saurin mayar da martanin da Gwamnan ya yi sa’o’i kadan bayan faruwar lamarin na nuna matukar damuwarsa kan halin da al’ummar jihar ke ciki.

 

Ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Neja game da mutuwar da aka yi tare da bukatar wadanda suka rasa ‘yan uwansu da su dauki wannan rashi kaddara daga Ubangiji, yana mai cewa mutuwa za ta iya zuwa ta kowace hanya kuma a kowane hali.

 

Venerable Daniel Tsado wanda kuma shi ne Mataimakin Cocin St Peter’s Anglican na Gbaiko a karamar hukumar Bosso, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon fashewar a ranar Asabar.

 

Ya kuma yi bayanin cewa daukacin Coci-coci na jihar suna bakin ciki kan wannan mummunan lamari tare da jajanta wa Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago kan rasuwar da aka samu.

 

Shugaban ya kuma tabbatar da kudurin CCN reshen jihar Neja na goyon bayansu ga manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Gwamna Bago don cimma sabuwar ajandar Neja.

 

Ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa matakin da ta dauka na daukar nauyin biyan kudaden jinya ga wadanda abin ya shafa da ke cikin mawuyacin hali da aka tura zuwa Abuja, baya ga matakin da ta dauka na kafa wani kwamiti mai karfi da zai binciki musabbabin faruwar lamarin.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara