Connect with us

Labarai

Bellingham Ya Zama Gwarzon Wasan La Liga Na Bana

Published

on

An zaɓi ɗan ƙwwallon Real Madrid, Jude Bellingham a matsayin gwarzon ɗan wasan La Liga na bana a kakar farko da ya yi a Sifaniya.

Bellingham, mai shekara 20, ya ci ƙwallo 19 a babbar gasar tamaula ta Sifaniya, wanda ya taimaka Real Madrid ta lashe kofin bana kuma na 36 jimilla.

Ƙungiyar Santiago Bernabeu ta kare a matakin farko a teburin gasar da tazarar maki 10 tsakaninta da Barcelona ta biyu mai rike da La Liga na bana.

Haka kuma ɗan wasan tawagar Ingila, ya zura ƙwallo hudu a raga a Champions League, inda ƙungiyar da Carlo Ancelotti ke jan ragama ta kai wasan karshe a bana.

RanarAsabar 1 ga watan Yuni Real Madrid za ta fafata da Borussia Dortmund a wasan karshe a gasar ta zakarun Turai.

Tsohon ɗan ƙwallon Dortmund ya yi takarar gwarzon dan wasan La Liga a bana tare da takwaransa, Vinicius Jr da Antoine Griezmann na Atletico Madrid da Artem Dovbyk na Girona da kuma Robert Lewandowski na Barcelona.

Ƙyaftin din ƙungiyoyin dake buga La Liga ne ke yin zaben tare da magoya baya da mahukuntan dake gudanar da ƙyautar.

Bellingham ne ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan Bundesliga a 2022/23 a lokacin da yake taka leda a Dortmund, daga baya Real Madrid ta dauke shi kan  kudi Fan miliyan tamanin da takwas da dubu dari biyar kafin fara kakar da aka kammala.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara