Connect with us

Labarai

Ba Gudu Ba Ja Da Baya Kan Zanga-Zangar Gama-Gari Da Za Mu Gudanar — NLC

Published

on

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta sanar da cewa babu gudu babu ja da baya dangane da zanga-zangar gama-gari da za ta gudanar a ranar 27 da 28 ga wannan wata na Fabarairu.

Sanarwar dai martani ce ga Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS)da ta bukaci kungiyar kwadagon ta sauya tunani kan zanga-zangar da a cewarta babu lallai ta wanye lafiya ba.

a safiyar wannan Larabar ce DSS ta yi kira ga kungiyar kwadagon da ta jingine shirinta na gudanar da zanga-zanga domin ci gaba da wanzuwar zaman lafiya da walwalar jama’a.

Gargadin DSS na zuwa ne tun bayan da a Juma’ar da ta gabata, NLC ta ayyana zanga-zangar kwanaki 2 a fadin kasar nan kan halin matsin da ‘yan Najeriya ke fuskanta da kuma matsalar tabarbarewar harkokin tsaro a fadin kasar.

Sanarwar ta kara da cewar gwamnatoci a dukkanin matakai na iya bakin kokarinsu wajen rage radadin halin kuncin da ake ciki, don haka ya kamata a kyautata musu zato.

Sai dai da ya ke martani kan wannan gargadi na DSS, Shugaban NLC Joe Ajaero, ya ce maimakon yi wa kungiyarsu barazana, kamata ya yi DSS ta daura damarar kama duk wadanda za su kawo hargitsi a yayin zanga-zangar.

A cewar Kwamared Ajaero, tarihi ba zai taba yafe wa ƙungiyar ƙwadago ba ma damar ta zauna ta yi shiru kuma ta nade hannu alhali ’yan Najeriya na ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa ba.

Shugaban kungiyar kwadagon, wanda ya bayyana matakin da ke tafe a matsayin “zanga-zangar lumana kan tsadar rayuwa da ba za a lamunta ba,” ya kara da cewa kungiyar kwadagon ba za ta nade hannunta ba yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da rayuwa cikin kunci.

“Muna so DSS ta sani cewa babu inda aka taba samun tashin hankula a zanga-zagar lumana da kungiyar kwadago ta taba gudanarwa, don haka batun mu janye wannan bai taso ba.”

Shugaban NLC ya koka kan yadda tattalin arzikin kasar ya tabarbare yana mai cewa yanzu haka darajar naira ta kara kundunbala inda farashinta a kasuwar canjin kudi ya kai N1,900 kan kowacce dalar Amurka daya.

Ya ba da tabbacin cewa babu wanda ya ke son ci gaban Najeriya kamar kungiyar kwadago kuma ba za ta taba yin wani abu da zai jawo rashin zaman lafiya ba.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara