Labarai
Azumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dakta Builder Muhammad Uba, ya kaddamar da rabon tallafin kudi domin taimaka wa marasa galihu a yankin yayin watan Ramadan mai alfarma.
Da yake jawabi a lokacin rabon tallafin, Dakta Muhammad Uba ya bayyana cewa an zabo wadanda suka amfana daga dukkanin kananan hukumomi 11 na Birnin Kudu.

Ya kara da cewa, jimillar mutane 110 sun karbi naira 20,000 kowannensu, yayin da wasu mutane 50 kuma suka karbi naira 50,000 kowannensu, domin rage radadin halin da iyalai da daidaikun mutane ke ciki a wannan wata na Ramadan.
A cewarsa, shirin na da nufin rage wa al’umma radadin matsin tattalin arziki a lokacin Ramadan.

Ya kuma bukaci wadanda suka amfana da tallafin da su yi amfani da kudaden yadda ya dace.
Dakta Muhammad Uba ya nuna godiya ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, bisa kokarinsa na tabbatar da jin dadin al’ummar jihar.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun bayyana godiyarsu ga shugaban karamar hukumar, inda suka ce wannan tallafi ya zo a kan lokaci.
Sun kuma yi addu’ar fatan alheri da samun nasara ga shugaban karamar hukumar da kuma Gwamna Umar Namadi.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoHukumar Alhazai ta Jigawa ta Jinjinawa Hukumomin Tsaro Bisa Goyon Bayan da Suke Ba Ta
