Connect with us

Labarai

An Kaddamar Da Kwamatin Inganta Ayyukan Samar Da Jini Ga Marasa Lafiya A Kano

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da kwamitin kwararru na jihar kan batun karin jini domin magance gibi da kalubalen da ke tattare da ayyukan karin jini.

Babban manufar kwamitin ita ce tabbatar da yin ƙarin lafiyayyen jini fa marasa lafiya a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar Labaran Yusuf ne ya kaddamar da kwamitin, inda ya bayyana cewa kafa kwamitin na da matukar muhimmanci wajen kare kamuwa da wata cuta sakamakon karin jini.

Ya kuma jaddada cewa an zabi ‘yan kwamitin ne bisa cancanta da kwarewarsu.

Kwamitin yana da alhakin samar da kwararru masana kula da lafiyar jini, da masu bada shawarwari kan lamarin, da haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki don haɓaka ayyukan ƙarin jini.

Kwamitin ya ƙunshi wakilai daga cibiyoyin kiwon lafiya daban-daban, waɗanda suka haɗa da Hukumar Kula da Asibitoci, da  Hukumar Kula da Cibiyoyin Kiwon Lafiya Masu Zaman Kansu, da Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko, da Hukumar Samar da Magunguna.

Hakavkuma akwai wakilai daga cibiyoyin ilimi, kamar Jami’ar Bayero Kano da Asibitin koyarwa na Aminu Kano.

Sakatariyar kwamitin, Dokta Hauwa Ibrahim, kwararra kan al’amuran da suka shafijini, za ta kasance mai bada shawarwari ga kwamitin.

Kwamitin yana da ‘yancin yin haɗin gwiwa tare da ƙarin masu ruwa da tsaki kamar yadda ake buƙata.

Kaddamar da kwamatin wani muhimmin mataki ne na inganta ayyukan samar da jini a jihar Kano, tare da tabbatar da tsaro da jin dadin majinyatan da aka yi musu karin jini.

 

Daga Khadija Aliyu

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara