Labarai
An Kaddamar Da Kwamatin Inganta Ayyukan Samar Da Jini Ga Marasa Lafiya A Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da kwamitin kwararru na jihar kan batun karin jini domin magance gibi da kalubalen da ke tattare da ayyukan karin jini.
Babban manufar kwamitin ita ce tabbatar da yin ƙarin lafiyayyen jini fa marasa lafiya a jihar.
Kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar Labaran Yusuf ne ya kaddamar da kwamitin, inda ya bayyana cewa kafa kwamitin na da matukar muhimmanci wajen kare kamuwa da wata cuta sakamakon karin jini.
Ya kuma jaddada cewa an zabi ‘yan kwamitin ne bisa cancanta da kwarewarsu.
Kwamitin yana da alhakin samar da kwararru masana kula da lafiyar jini, da masu bada shawarwari kan lamarin, da haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki don haɓaka ayyukan ƙarin jini.
Kwamitin ya ƙunshi wakilai daga cibiyoyin kiwon lafiya daban-daban, waɗanda suka haɗa da Hukumar Kula da Asibitoci, da Hukumar Kula da Cibiyoyin Kiwon Lafiya Masu Zaman Kansu, da Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko, da Hukumar Samar da Magunguna.
Hakavkuma akwai wakilai daga cibiyoyin ilimi, kamar Jami’ar Bayero Kano da Asibitin koyarwa na Aminu Kano.
Sakatariyar kwamitin, Dokta Hauwa Ibrahim, kwararra kan al’amuran da suka shafijini, za ta kasance mai bada shawarwari ga kwamitin.
Kwamitin yana da ‘yancin yin haɗin gwiwa tare da ƙarin masu ruwa da tsaki kamar yadda ake buƙata.
Kaddamar da kwamatin wani muhimmin mataki ne na inganta ayyukan samar da jini a jihar Kano, tare da tabbatar da tsaro da jin dadin majinyatan da aka yi musu karin jini.
Daga Khadija Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
