Connect with us

Ilimi

An Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman Gumel, ya bayyana sabon Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Farfesa Ahmad Muhammed Gumel, a matsayin mutum mai son kawo cigaba ga al’ummarsa.

Mataimakin Gwamnan ya bayyana hakan ne a wurin liyafar karramawa da abokan Farfesa Gumel suka shirya masa a dakin taro na masarautar Gumel.

A cewarsa, bai yi mamakin yadda jama’a suka halarci bikin rantsar da Shugaban Jami’ar a Dutse da kuma liyafar da aka yi masa a Gumel ba, domin sabon Shugaban Jami’ar mutum ne mai kula da jama’a, abokan aikinsa da duk wanda ya taɓa hulɗa da shi.

Ya kuma bayyana cewa a lokacin da Farfesa Gumel yake ƙasar Malaysia, ya taimaka wajen samar wa da dama daga cikin mutanensa guraben karatu da tallafin karatu.

 

Ya buƙaci sabon Shugaban Jami’ar da ya kasance mai aiki bisa gaskiya, tare da yin adalci ga kowa, yana mai cewa yana da yaƙinin  zai yi nasara a Jami’ar Tarayya da ke Dutse.

Dr. Najib Abdulhamid, wanda ke aiki da Microsoft Office a ƙasar Kenya, ya yi magana a madadin abokan sabon Shugaban Jami’ar, inda ya ce suna farin cikin ganin abokinsu tun daga yarinta ya kai kololuwar matsayinsa na aiki, kuma za su tallafa masa da addu’o’i da shawarwari domin ya zamto abin tunawa a tarihin jami’ar.

Ya ce sun yi nazari sosai kan tsare-tsarensa guda goma sha ɗaya, kuma suna da yaƙinin cewa zai  mayar da hankali, jajircewa da kuma samun ƙwararrun ma’aikata, domin cimma manufofinsa, ya ce za kuma su yi amfani da alaƙarsu wajen taimaka masa ya cimma burinsa ga jami’ar.

A nasa jawabin, Farfesa Muhammed Sani Gumel, tsohon Mataimakin Shugaban Jami’a mai kula da harkokin karatu a Jami’ar Bayero da ke Kano, ya taya sabon Shugaban Jami’ar murna tare da ba shi shawarar fahimtar dokokin jami’a sosai.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara