Connect with us

Ilimi

An Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman Gumel, ya bayyana sabon Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Farfesa Ahmad Muhammed Gumel, a matsayin mutum mai son kawo cigaba ga al’ummarsa.

Mataimakin Gwamnan ya bayyana hakan ne a wurin liyafar karramawa da abokan Farfesa Gumel suka shirya masa a dakin taro na masarautar Gumel.

A cewarsa, bai yi mamakin yadda jama’a suka halarci bikin rantsar da Shugaban Jami’ar a Dutse da kuma liyafar da aka yi masa a Gumel ba, domin sabon Shugaban Jami’ar mutum ne mai kula da jama’a, abokan aikinsa da duk wanda ya taɓa hulɗa da shi.

Ya kuma bayyana cewa a lokacin da Farfesa Gumel yake ƙasar Malaysia, ya taimaka wajen samar wa da dama daga cikin mutanensa guraben karatu da tallafin karatu.

 

Ya buƙaci sabon Shugaban Jami’ar da ya kasance mai aiki bisa gaskiya, tare da yin adalci ga kowa, yana mai cewa yana da yaƙinin  zai yi nasara a Jami’ar Tarayya da ke Dutse.

Dr. Najib Abdulhamid, wanda ke aiki da Microsoft Office a ƙasar Kenya, ya yi magana a madadin abokan sabon Shugaban Jami’ar, inda ya ce suna farin cikin ganin abokinsu tun daga yarinta ya kai kololuwar matsayinsa na aiki, kuma za su tallafa masa da addu’o’i da shawarwari domin ya zamto abin tunawa a tarihin jami’ar.

Ya ce sun yi nazari sosai kan tsare-tsarensa guda goma sha ɗaya, kuma suna da yaƙinin cewa zai  mayar da hankali, jajircewa da kuma samun ƙwararrun ma’aikata, domin cimma manufofinsa, ya ce za kuma su yi amfani da alaƙarsu wajen taimaka masa ya cimma burinsa ga jami’ar.

A nasa jawabin, Farfesa Muhammed Sani Gumel, tsohon Mataimakin Shugaban Jami’a mai kula da harkokin karatu a Jami’ar Bayero da ke Kano, ya taya sabon Shugaban Jami’ar murna tare da ba shi shawarar fahimtar dokokin jami’a sosai.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara