Ilimi
An Bukaci Musulmi Su Kula da Maganganunsu
An shawarci Musulmi da su kula da maganganunsu tare da tabbatar da cewa suna faɗar gaskiya a kowane lokaci.
Limamin Masallacin Darul-Khair da ke Ilorin, Jihar Kwara, Imam Abdulmumini Abdulrafiu-Onilaru ne ya yi wannan kira a yayin hudubar Juma’a.
Ya bayyana cewa mutane da dama na amfani da maganganunsu wajen jawo wa kansu da kuma wasu cutarwa.
A cewarsa, kasancewar ana cikin watan Rajab, ana sa ran Musulmi za su fara shirya kansu tun yanzu domin tunkarar watan azumin Ramadan.
Imam Abdulrafiu-Onilaru ya shawarci Musulmi da su rungumi dabi’ar aikata alheri a kowane lokaci, domin samun lada mai kyau daga Allah.
ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
