Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Published

on

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin aikin da suke gudanarwa, domin bai wa tattaunawa damar ci gaba don warware matsalolin da ke haddasa rikicin cikin gaggawa.

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mista Peter Ahemba, ne ya yi wannan roko yayin da yake jawabi ga ’yan jarida a taron manema labarai na watanni biyu-biyu da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Mista Ahemba ya ce yajin aikin da Malaman Kwalejin Ilimi ta Akwanga da kwalejin kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai Lafia, da Kwalejin Aikin Noma, Kimiyya da Fasaha ta Lafia ke yi na iya kawo cikas ga karatun dalibai. Saboda haka, ya roki ƙungiyoyin malaman da su koma teburin tattaunawa domin cimma matsaya cikin lumana.

Ƙungiyoyin Malaman Manyan Makarantu na Jihar Nasarawa sun ayyana yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar 29 ga Disamba, 2025, bisa rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa ga mambobinsu.

Babban Mataimakin na Musamman ya bayyana cewa kwanan nan Gwamna Abdullahi Sule ya raba katifa dubu ɗaya da gadaje ga daliban Kwalejin Ilimi ta Akwanga (COEA), domin inganta muhallin koyo da koyarwa.

Ya ce wannan rabon na daga cikin kulawar da gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule ke bai wa fannin ilimi tun daga lokacin da ta hau mulki a shekarar 2019.

Mista Ahemba ya ƙara da cewa gwamnatin ta gina azuzuwa da dama, ta gyara makarantu masu yawa, tare da gina katangar kariya a makarantu da dama domin kare su daga mamaya.

Ya kuma ce gwamnatin ta fahimci yadda wasu miyagun mutane ke shiga jihar a hankali, lamarin da ke barazana ga tsaron mazauna yankin.

Mista Ahemba ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin tsakar dare da wasu da ba a tantance su ba suka kai wa mazauna Akunza da ke yankin Ashige a karamar hukumar Lafia.

Ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnati na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki wajen aiwatar da sabbin matakan tsaro domin shawo kan irin waɗannan hare-hare.

Ya kuma yi kira ga ’yan ƙasa da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen kama masu aikata laifuka a dukkan sassan jihar.

Mista Ahemba ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Saboda haka, ya roki jama’a da su rika kai rahoton duk wani abu da suke zargin ba daidai ba ga hukumomin da suka dace, tare da ba da cikakken haɗin kai ga jami’an tsaro domin hana aikata laifuka da yaki da su.

COV: Aliyu Muraki / Lafia

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara