Kasuwanci
An Bukaci Manoman Kano Su Shiga Baje Kolin Kayan Noma Na Kasa
Hukumar Noma da Raya Karkara ta Jihar Kano (KNARDA) ta yi kira ga manoma da masu ruwa da tsaki a harkar noma da masu kirkire-kirkire a jihar da su shiga baje kolin noma na kasa da ke tafe.
A cikin wata sanarwa da Sashen Kula da Ayyukan Yada Labarai, KNARDA ya fitar, ta bayyana taron a matsayin wani babban dandali na baje kolin kayayyakin amfanin gona, da fasahohin zamani, da ke inganta samar da abinci da raya karkara.
Hukumar ta ja hankalin daidaikun jama’a da kungiyoyi a Kano da su yi amfani da wannan damar wajen gabatar da nasarorin da suka samu da kuma gano sabbin hanyoyin kasuwanci a fannin noma.
KNARDA ta kuma jaddada aniyar ta na tallafawa kokarin da ke inganta ayyukan noman zamani da ci gaban karkara.
Abdullahi Jalaluddeen/Kano
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
