Connect with us

Ilimi

Ambaliyar Ruwa Ta Haifar Da Koma-baya A Fannin Ilimi A Najeriya-UNICEF

Published

on

Daga cikin yara ‘yan makaranta miliyan 242 da matsanancin yanayi ya raba da muhallansu a kasashe 85 a shekarar 2024, dalibai  miliyan 2 da dubu 200 ne a Najeriya suka rabu da muhallansu, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin ilimi a shekarar.

Rahoton wanda Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya fitar a daidai lokacin da duniya ke bikin ranar ilimi ta duniya ta shekarar 2025, ya nuna cewa a Najeriya baki daya dalibai miliyan 2,200,200 ne suka daina makaranta sakamakon ambaliyar ruwa.

Da take gabatar da jawabi kan tasirin da sauyin yanayi ke da shi ga ilimin yara, shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Farah ya bayyana cewa, ambaliyar ruwa da ta afku a jihar Jigawa a shekarar da ta gabata ta lalata gine-ginen makarantu 115, wanda hakan ya kawo cikas ga  dalibai.

Ya bayyana alhininsa kan yadda lamarin ya haifar da tsawaita rufe makarantu,  wanda ya shafi karatun  yara sama da 92,518 a fadin kananan hukumomi 27 na jihar.

A jihar Jigawa, ambaliyar ruwan da ta afku a shekarar da ta gabata ta lalata  gine-gine da kayayyakin makarantu 115, wanda hakan ya sa ba za a iya amfani da su ba.

“Hakan ya haifar da tsawaita rufe makarantu da kuma rashin wadatar ilimi ga dalibai kimanin 92,518, wadanda 43,813 daga cikinsu mata ne, yayin  da 48,705 kuma yara maza ne, a fadin kananan hukumomi 27 na jihar,” Mista Farah.

Ya yi nuni da cewa, UNICEF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin kasashen waje da na kungiyar kasashen renon Ingila da ke  Burtaniya, na tallafa wa gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa, don samar da yanayin koyo mai kyau domin rage tasirin sauyin yanayi da ya shafi koyon ilimia makarantu.

Ya bayyana cewa, a shekarar 2024, UNICEF ta dauki nauyin matasa dubu daya, wadanda 350 daga cikinsu sun fito ne daga jihar  Jigawa, yayin da 650 kuma suka fito daga Katsina, don dasa bishiyu 300 a yankin hamada da kuma wuraren da ake fama da ambaliyar ruwa a jihohin biyu, domin dakile tasirin sauyin yanayi.

Tare da goyon bayan abokan hulda da suka hada da ofishin kula da harkokin kasashen waje, da na kungiyar kasashen renon Ingila da ke Birtaniya, UNICEF na tallafawa jihohin Kano da Jigawa don samar da yanayin koyo mai kyau, don rage tasirin da  sauyin yanayi ke haifarwa”. 

Shugaban na UNICEF ya kuma bayyana cewa a shekarar da ta gabata asusun ya gina cibiyoyin kula da tsaftar ruwa da tsaftar muhalli (WASH) a makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya a wuraren da ake bukata a cikin jihohin uku.

Ya ce asusun ya kuma gina tare da gyara wuraren tsaftar muhalli a makarantu 33, inda aka gina 25 a jihar Kano, sauran 8 kuma a jihar Jigawa, wadanda yara 39,432 ke amfani da su a jihohin biyu.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara