Connect with us

Labarai

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Published

on

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru.

Malam Suleiman Lawal, mai shekaru 78, ya rasu a daren Asabar, 3 ga Janairu, 2026, bayan fama da doguwar jinya.

Kafin rasuwarsa, ya kasance Sakataren Kwamitin Aiki da cikawa (Task Force Committee) kan gina Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH), Shika, Zariya, da kuma Cibiyar kula da lafiyar Ido ta Ƙasa (National Eye Center), Kaduna.

A baya, ya riƙe muhimman mukamai da dama, ciki har da shugaban Kwalejin Fasaha ta Jihar Kaduna dake Zariya (wacce yanzu ake kira Nuhu Bamalli Polytechnic, Zariya), Kwamishinan Tarayya a Hukumar kula da da’ar Ma’aikata Federal Character Commission mai wakiltar Jihar Kaduna, da kuma Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, da sauransu.

Marigayi Jarman Kauru ya rasu ya bar mata biyu, ’ya’ya 14, da jikoki da dama.

Daga cikin ’ya’yansa akwai Alhaji Nuraddeen Suleiman Lawal Mayana Kauru, Sakataren Ilimi (Academic Secretary) na kwalejin kimiyya da fasaha ta Nuhu Bamalli, Zariya.

An gudanar da sallar jana’izan sa a Filin Eid na Mallawa da ke Ban Zazzau, Zariya, da misalin karfe 1:30 na rana, Lahadi, 4 ga Janairu, 2026.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa kurakuransa, Ya kuma ba shi Aljannar Firdausi.

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara