Connect with us

Labarai

Hajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa tace ta dawo da ci gaba da bitar maniyyatan aikin hajjin bana a dukkan kananan hukumomin jihar bayan kammala azumin watan Ramadan.

Daraktan Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala ganawa da manyan jami’an hukumar a Dutse babban birnin jihar.

Yana mai cewar, hukumar da dakatar da bitar ne saboda azumin watan ramadan.

A don haka, a zancen da ake yi yanzu, an dawo da bitar maniyyatan gadan-gadan domin kara fadakar da su gami da ilmantar da su yadda za su gudanar da aikin hajji a kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma bukaci maniyyata da su tashi tsaye wajen ganin sun samu ilimin aikin hajji domin samun damar yin aikin hajji karbabbe.

Yayi nuni da cewar, hukumar ta kammala shirye-shiryen tantance lafiyar maniyyata, wanda hakan ya sanya hukumar aikin hajji ta kasa ta jinjina wa tsarin jihar Jigawan, kuma ta farko wajen yin hakan.

Labbo, ya kara da cewar hukumar za ta yi zama na musamman da shugabannin shiyoyinta na jihar da kuma jami’anta na kananan hukumomi wato center officers domin tattauna muhimman batutuwa da suka shafi tsarin fara jigilar maniyatan daga nan gida zuwa ƙasa mai tsarki.

Ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi, bisa goyon bayan da yake ba su domin ganin jihar ta ci gaba da zama ta ɗaya a gudanar da aikin hajji.

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara