Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar.

An gudanar da bikin rantsarwar a Fadar Shugaban Ƙas, inda Shugaba Tinubu ya taya sabon ministan murna, tare da bayyana kwarin gwiwarsa kan cewa zai  taimaka wajen aiwatar da manufofin gyaran tattalin kasa.

Shugaban ƙasar ya yaba wa Oyedele kan rawar da ya taka wajen jagorantar kokarin gyara tsarin haraji na Najeriya, inda ya bayyana cewa tsohon tsarin harajin ƙasar ya tsufa kuma yana bukatar sabuntawa domin ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana.

A nasa jawabin, sabon Ministan ya gode wa Shugaban ƙasa bisa amincewar da ya nuna masa, yana mai cewa damar da aka ba shi ta yi wa ƙasa hidima babbar abar alfahari ce.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa zai ba da dukkan ƙoƙarinsa wajen gudanar da aikinsa, yana mai cewa manufofin kudin gwamnati za su mayar da hankali kan ƙarfafa tattara kudaden shiga, inganta yadda ake kashe kuɗi, da kuma tabbatar da dorewar tattalin arzikin ƙasa.

Labarai

Labarai14 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai18 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai22 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai23 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara