Labarai
Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar asalin jihar, Walida Abdulhadi, har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi adalci.
Gwamnan ya bayar da wannan tabbaci ne a ranar Laraba lokacin da ya gana da iyayen Walida tare da lauyansu a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
A yayin ganawar, gwamnan ya yi wa iyayen bayani kan halin da Walida ke ciki a halin yanzu, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da kula da lafiyar ta, ci gaba da karatunta da kuma kula da walwalarta gaba ɗaya.
Ya bayyana cewa a halin yanzu Walida na karɓar kulawar jinya a wani asibiti da Gwamnatin Jigawa ke ɗaukar nauyin kuɗaɗensa, yana mai cewa bayan kammala wannan kulawa, za a mayar da ita cikin iyalanta.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa an riga an tura ƙwararrun ma’aikatan kula da walwalar al’umma domin ba Walida da jaririnta kulawa ta musamman, yana mai jaddada cewa an tanadi dukkan matakan tallafi da suka dace domin kare lafiyarta da tabbatar da ganin ta murmure.
Bugu da ƙari, Gwamna Namadi ya ce gwamnatin jihar za ta mayar da Walida makaranta tare da ɗaukar nauyin karatunta gaba ɗaya domin ta ci gaba da neman ilimi ba tare da wata tangarda ba.
Da yake bayyana lamarin a matsayin satar mutane kai tsaye, gwamnan ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da an yi adalci ta hanyoyin shari’a da suka dace, kuma duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi bisa doka.
Haka kuma ya sanar da cewa gwamnati za ta tallafa wa Walida da iyalanta domin inganta rayuwarsu da taimaka musu su sake farfaɗo da rayuwarsu.
Gwamna Namadi ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Jihar Jigawa na kare haƙƙoƙi da mutuncin dukkan ‘yan jihar a duk inda suke.
Da yake magana a madadin iyayen Walida, lauyanta Barrista Kabiru Adamu ya gode wa Gwamna Namadi bisa saurin ɗaukar matakin ceto yarinyar da kuma ƙoƙarin gwamnati na ganin an dawo da martabar ta.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai5 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
