Connect with us

Labarai

NSCDC Ta Tura Jami’ai Sama da 2000 Kananan Hukumomin Jihar Kaduna Gabanin Bukukuwan Kirsimeti

Published

on

Daga Usman Sani

Kwamandan Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Civil Defence (NSCDC) a Jihar Kaduna, Panam Musa Buba, ya bayar da umarnin tura jami’an tsaro a dukkan kananan hukumomi ashirin da uku na jihar.

A wannan karo, ya umurci a tura jami’ai dubu biyu da ɗari (2,100) domin tabbatar da tsaron al’umma a lokacin bukukuwan ƙarshen shekara.

Wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar jihar, SC Habeeb Badamasi, ya fitar, ta bayyana cewa an daukin matakin hakan ne da nufin ƙarfafa tsaro kafin Kirsimeti, da lokacin Kirsimetin da bayan bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

Kwamandan Panam Musa Buba ya tabbatar wa mazauna jihar cewa za su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum cikin kwanciyar hankali, inda ya jaddada ƙudurin rundunar wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a tsawon lokacin bukukuwan.

Mun zo ne domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro, domin kowa ya more wannan lokaci na bukukuwa cikin natsuwa,” In ji shi.

Haka kuma, ya gargaɗi masu aikata laifuka da su janye daga duk wani shiri na aikata laifi, yana mai bayyana cewa jami’an NSCDC tare da sauran hukumomin tsaro za su kasance a wurare masu muhimmanci domin hana aikata laifuka.

Jami’anmu sun shirya tsaf, a don haka, duk wanda ya zabi aikata laifi zai fuskanci hukunci mai tsauri,” in ji Kwamandan.

Kwamandan Panam Buba ya kuma bukaci al’ummar Kirista da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwa wajen tunani da nazari kan ainihin ma’anar Kirsimeti.

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara