Ilimi
Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi
Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya reshen Jihar Kebbi ta tabbatar da sace dalibai ashirin da biyar daga Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata ta Gwamnati da ke Maga a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu.
Lamarin ya faru ne a daren Litinin da misalin ƙarfe 4 na safe a lokacin da ƴan bindiga suka mamaye makarantar, inda suka kashe wani ma’aikaci ɗaya tare da jikkata wani.
A cewar wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan, CSP Nafi’u Abubakar Kotarkoshi ya sanya wa hannu, maharan ɗauke da makamai masu ƙarfi sun kutsa makarantar inda suka yi musayar wuta da jami’an tsaro da ke bakin aiki. Duk da ƙoƙarin jami’an, an ruwaito cewa maharan sun haye katangar makarantar suka kuma yi awon gaba da ɗaliban daga ɗakunan kwanan su.
Jami’in ya tabbatar da cewa Hassan Makuku wanda rahotanni suka ce shi ne mataimakin shugaban makarantar ya rasa ransa yayin harin, yayin da wani Ali Shehu ya samu rauni sakamakon harbinsa da bindiga a hannunsa na dama.
Bayan faruwar lamarin, sanarwar ta ce Kwamishinan ‘Yan Sanda, Bello Muhammad Sani, ya tura jami’an ‘yan sanda na musamman tare da jami’an soji da ƙungiyoyin ‘yan bijilanti zuwa yankin.
Tawagar haɗin gwiwa na ci gaba da bincike a hanyoyin da ake zargin maharan sun bi da dazuzzukan da ke kewaye domin gudanar da aikin ceto da kuma kama waɗanda suka aikata laifin.
Kwamishinan ya yi kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da kasancewa masu lura da muhallinsu, yana tabbatar musu da cewa rundunar za ta ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.
Sani Haruna Dutsinma
-
Labarai2 days agoGwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah
-
Labarai7 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai7 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
-
Labarai7 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai5 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai5 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai5 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai5 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
