Labarai
Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Dillalin Makamai A Taraba
A ci gaba da aikace-aikacen yaki da ta’addanci da laifuffuka a fadin Jihar Taraba karkashin Operation Lafiya Nakowa, sojojin Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya / Sashen 3 na Operation Whirl Stroke (OPWS) sun samu nasarar kama wani wanda ake zargin dillalin makamai, tare da kwato makamai da harsasai daga hannunsa.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Lieutenant Muhammad, Mai Rikon Mukamin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar 6, ya sanya wa hannu.
A cewar sanarwar, bisa sahihan bayanan leƙen asiri da aka samu, a ranar 12 ga Nuwamba, 2025, sojojin suka kai samame a kauyen Shagada, karkashin gundumar Namnai a Karamar Hukumar Gassol, Jihar Taraba. Samamen ya haifar da kama wani mutum mai suna Abdulmudallabi Audu, mai shekaru 25, wanda aka same shi da makamai da harsasai.
Kayan da aka gano daga hannun wanda ake zargin sun haɗa da Bindiga samfurin AK-47 guda ɗaya da kurtun harsasai AK-47 guda biyu da kuma Harsasai guda 53 masu tsawo mita kusan 8.
A yanzu haka, wanda ake zargin tare da kayan da aka kwato suna tsare a hedkwatar Runduna ta 6 domin bincike da shirin gurfanarwa a kotu.
Kwamandan Rundunar 6, Brigadier Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin bisa ƙwarewa, jajircewa, da saurin mayar da martani ga bayanan sirri da ake samu.
Janar Uwa ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aikace-aikace masu ƙarfi a duk fadin Taraba domin tabbatar da zaman lafiya, tsaro, da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a Arewa maso Gabas da yankunan makwabta.
Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da bayanai sahihai akan lokaci ga jami’an tsaro domin taimakawa wajen kassara masu aikata laifuka da farfaɗo da cikakken zaman lafiya a jihar.
Sani Sulaiman/Jalingo
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
