Kasuwanci
Minista Matawalle ya Karɓi Manyan Jiga-Jigan PDP Da Suka Koma Jam’iyyar APC
Aƙalla shugabanni 15 na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Jihar Zamfara sun sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC).
An gabatar da waɗannan waɗanda suka sauya shekar ne a gaban Ministan Harkokin Tsaro na Ƙasa, Dr. Bello Mohammed Matawalle, a Abuja ranar Laraba, ta hannun Shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Umar Danfulani, tare da Sanata Tijjani Yahaya Kaura da Alhaji Lawal M. Liman.
A cewar wata sanarwa da Mai Magana da yawun jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, Yusuf Idris Gusau, ya fitar, Minista Matawalle ya tarbi sabbin ’yan jam’iyyar da farin ciki, inda ya tabbatar musu da daidaito da damar ci gaba da aiki a cikin jam’iyyar.
Dr. Matawalle ya bayyana matakin da suka ɗauka na komawa APC a matsayin abin jarumtaka kuma daidai da lokaci, tare da nuna farin ciki kan yadda jam’iyyar ke ƙara samun karɓuwa a Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya.
Ya yaba wa shugabannin jam’iyyar a matakin jiha bisa jajircewar su wajen tuntuba da wayar da kan jama’a, wanda ya ce hakan ya ƙarfafa martabar APC a sassan jihar.
Da yake gabatar da waɗanda suka sauya sheka, Shugaban APC na Jihar Zamfara, Tukur Umar Danfulani, ya bayyana cewa sabbin ’yan jam’iyyar sun haɗa da manyan shugabanni 15 na PDP a matakin jiha da yankuna, waɗanda suka shiga APC domin shirye-shiryen zaɓen 2027.
Ya ce an karɓe su tun da farko ta hannun Sanata Tijjani Yahaya Kaura, a madadin tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar Zamfara ta Yamma, Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar.
Daga cikin fitattun waɗanda suka sauya sheka akwai: Isiyaka M. Dabo, Shugaban Matasa na PDP; Nasiru Mohammed Anka, Ma’ajin Yankin Zamfara ta Yamma; Junaidu Magaji Kiyawa, Sakataren Shirye-shirye na PDP na Zamfara ta Arewa; Musa Halilu Faru, Mataimakin Sakataren Shirye-shirye na Zamfara ta Yamma; Alhaji Lawali Aliyu Shinkafi, Sakataren Yanki na Zamfara ta Arewa; da kuma Hajiya Rabi Bakura da Hajiya Amina Duniya, waɗanda duka Ex-Officio ne na PDP a matakin jiha.
Sauran sun haɗa da Bashar Mohammed Dogon Kade, tsohon ɗan takarar majalisar jiha ta Kaura Namoda South, da Rilwanu Bello, tsohon ɗan takarar kansila.
Shi ma Sanata Tijjani Kaura, ya bayyana wannan sauya sheka a matsayin babban abin farin ciki ga APC, yana mai cewa sabbin mambobin za su ƙara ƙarfafa ginin jam’iyyar da kyautata damar ta a gaban zaɓen 2027.
Ita kuwa Hajiya Amina Duniya, wacce ta ce ta shafe shekaru 25 a jam’iyyar PDP, ta yi alkawarin jawo ƙarin magoya baya zuwa APC tare da kira da a tabbatar da adalci da daidaito ga kowa.
Taron ya samu halartar manyan jiga-jigan APC da suka haɗa da: Hon. Lawal M. Gabdon Kaura, tsohon shugaban APC; Alhaji Kabiru Balarabe, tsohon Sakataren Gwamnati; Hon. Yazid Shehu Danfulani, Manajan Darakta na NIAC; Barr. Aminu Junaidu, tsohon Kwamishinan Shari’a; Alhaji Sha’ayau Yusuf Talata-Mafara; Hon. Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa; da Malam Yusuf Idris Gusau, Mai Magana da yawun jam’iyyar, da sauransu.
Aminu Dalhatu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
