Labarai
‘Yansandan Jihar Filato Zasu Koya Darasi Ga Masu Daukar Hukunci Ba Tare Da Bincike Ba
Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Filato, ta sha alwashin ba da misali da masu yanke hukunci da kansu ba tare da barin doka ta yi aikin ta ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Filato, CP Emmanuel Adesina ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Jos yayin da suka kama wasu manyan mutane tara (9) da ake zargi da hannu wajen garkuwa da mutane da wasu laifuka daban-daban.
Ku tuna cewa a wasu lokutan a cikin watan Agustan wannan shekara ta 2025, an kashe jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) a karamar hukumar Bassa sakamakon aikata irin wannan danyen aiki.
An bayyana cewa dan sandan ya tafi bakin aiki ne, inda ya zakulo wanda ake zargi da gudu sannan ya kama mai laifin, sai ya fara ihun barawo…. barawo….sai ga jama’a sun kashe jami’in har lahira ba tare da basu damar bayyana kansa ba.
Rundunar ‘yan sandan jihar Filato, CP, wadda ya yi kakkausar suka ga irin wannan aikin, ya ce sun kama mutane da dama da ake zargi da aikata laifin.
Ya kuma bayyana dalilin da ya sa aka kama wadanda ake zargi da yin garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a wurare daban-daban a fadin jihar.
Ya kuma bukaci ‘yan jihar Filato da su kasance masu taka-tsan-tsan tare da baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai masu inganci da za su bankado masu mugun nufi da jihar Filato da Najeriya baki daya.
DORCAS GWANI JOS.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
