Connect with us

Ilimi

Jigawa Za Ta Kafa Kananan Bankuna 5 A Wasu Sassan Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce ta amince da fara shirin karbar lasisin aiki don kafa sabbin Kananan bankunan guda 5 a wasu wurare da aka zaba a fadin jihar.

 

Kwamishinan yada labarai na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

 

A cewarsa, shirin wani bangare ne na dabarun gwamnatin jihar na fadada hanyoyin samar da kudade da zurfafa shiga harkokin tattalin arziki a yankunan karkara da marasa galihu.

 

Ya bayyana cewa, za a kafa bankunan masu karamin karfi a kananan hukumomin Birniwa, Gujungu – Taura, Guri, Gwaram da Kaugama.

 

Ya ce, shawarar da majalisar ta yanke ya nuna irin sadaukarwar da gwamnatin Gwamna Umar Namadi ta yi na bunkasa hada-hadar kudi a matsayin wani makami na rage radadin talauci, bunkasa sana’o’in cikin gida, da karfafa tattalin arziki daga tushe.

 

Sagir ya ci gaba da cewa, sabon tallafin kudi na da nufin karawa kananan bankunan jihar tallafi, da samar da ayyuka na kudi kamar tanadi, bashi, da tallafin kananan ‘yan kasuwa ga daidaikun jama’a da al’ummomin da a al’adance ke cire su daga tsarin banki na zamani.

 

Ya kuma bayyana cewa, majalisar ta kuma amince da bayar da kwangilar samar da lantarki ta amfani da hasken rana a muhimman cibiyoyin zamantakewar al’umma a jihar.

 

Ya ce, darajar kwangilar ta kai sama da naira miliyan 733, inda ya kara da cewa amincewar ya yi daidai da manufofin shirin samar da hanyoyin samar da hasken rana na jihar, wanda aka tsara shi don fadada wutar lantarki zuwa sassa masu muhimmanci kamar ilimi, kiwon lafiya, da sauran muhimman ababen more rayuwa a fadin Najeriya.

 

Kwamishinan ya ce, tsarin tantancewar fasaha da tsare-tsare zai samar da cikakken tantance bukatun makamashi, dacewa da kayayyakin more rayuwa, da kuma tsare-tsaren aiwatar da aikin shimfida tsarin hasken rana a zababbun makarantu, cibiyoyin kiwon lafiya, da sauran muhimman cibiyoyin gwamnati a fadin jihar Jigawa.

 

Ya kara da cewa, aikin na nuni da yadda gwamnatin Namadi ta kuduri aniyar samar da hanyoyin samar da makamashi mai dorewa, da samar da ababen more rayuwa masu jure yanayi, da kuma inganta ayyukan hidima a sassa masu muhimmanci.

 

KARSHE/USMAN MZ

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara