Labarai
Hukumar Alhazai Ta Birnin Tarayya Ta Bai Wa Alhazai Zabi
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Babban Birnin Tarayya Abuja ta bukaci maniyyatan da ke son a mayar musu da kudaden aikin Hajji da suka biya sakamakon karin da aka yi, da su gabatar mata da bukatar hakan.
Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Muhammad Lawal Aliyu ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.
Muhammad Aliyu ya ce Maniyyatan da suka riga suka biya Nera Miliyan Hudu da Dubu Dari Shida da Casa’in da Tara, za su cikasa Nera Miliyan Daya da Dubu Dari Tara da Goma sha Takwas nan da ranar 27 ga watan Maris 2024, domin samun damar gudanar da aikin Hajjin.
Hakan a cewarsa ya yi daidai da sabon umurnin da Hukumar Alhazai ta Kasa ta bayar.
“Don haka dukkan maniyyatan da suka riga suka biya kudi a baya, za su kara biyan kumanin Nera Milyan Biyu, yayin da wadanda ba su biya ko sisi ba, za su biya jimillar Nera Miliyan Takwas da Dubu Dari Biyu da Hamsin da Hudu kafin cikar wa’adin. “Inji shi.
Hukumar ta shawarci wadanda ke son a mayar musu da kudadensu da su rubuta bukatar hakan ga Daraktan hukumar ta babban birnin tarayya Abuja tare da bayanan asusun ajiyarsu na banki domin a dawo musu da kudaden, ko kuma su dage tafiyarsu zuwa shekara mai zuwa.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
