Labarai
Hukumar Alhazai Ta Birnin Tarayya Ta Bai Wa Alhazai Zabi
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Babban Birnin Tarayya Abuja ta bukaci maniyyatan da ke son a mayar musu da kudaden aikin Hajji da suka biya sakamakon karin da aka yi, da su gabatar mata da bukatar hakan.
Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Muhammad Lawal Aliyu ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.
Muhammad Aliyu ya ce Maniyyatan da suka riga suka biya Nera Miliyan Hudu da Dubu Dari Shida da Casa’in da Tara, za su cikasa Nera Miliyan Daya da Dubu Dari Tara da Goma sha Takwas nan da ranar 27 ga watan Maris 2024, domin samun damar gudanar da aikin Hajjin.
Hakan a cewarsa ya yi daidai da sabon umurnin da Hukumar Alhazai ta Kasa ta bayar.
“Don haka dukkan maniyyatan da suka riga suka biya kudi a baya, za su kara biyan kumanin Nera Milyan Biyu, yayin da wadanda ba su biya ko sisi ba, za su biya jimillar Nera Miliyan Takwas da Dubu Dari Biyu da Hamsin da Hudu kafin cikar wa’adin. “Inji shi.
Hukumar ta shawarci wadanda ke son a mayar musu da kudadensu da su rubuta bukatar hakan ga Daraktan hukumar ta babban birnin tarayya Abuja tare da bayanan asusun ajiyarsu na banki domin a dawo musu da kudaden, ko kuma su dage tafiyarsu zuwa shekara mai zuwa.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United