Kasuwanci
Gwamna Namadi Ya Sha Alwashin Kara Inganta Kasuwar Maigatari
Gwamnatin Jihar Jigawa ta tabbatar wa al’ummar ƙaramar hukumar Maigatari cewa kasuwar Maigatari za ta zama ɗaya daga cikin cibiyoyin kasuwanci a Najeriya.
Gwamna Umar Namadi ne ya bayar da tabbacin yayin da yake jawabi a taron sauraron jama’a da aka gudanar a Maigatari.


A cewarsa, jihar tana aiwatar da jerin ayyuka da nufin bunƙasa harkokin kasuwanci da kuma samar da ayyukan yi ga matasan da ba su da aikin yi.
Gwamnan ya duba aikin ginin ɗakin taro da shugaban ƙaramar hukumar Maigatari, Alhaji Muhammad Na’Allah ke yi, inda ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar Maigatari bisa aiwatar da manyan ayyuka.


Gwamna Namadi ya kuma kaddamar da ginin ajujuwa uku na makarantar firamare da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Gumel, Maigatari, Sule Tankarkar da Gagarawa, Nazifi Sani, ya gina a garin Maigatari.
Ya ƙara bayyana godiya ga jama’ar Maigatari bisa kyakkyawar karɓar da suka yi masa tare da tawagarsa a lokacin ziyarar.


Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamna Malam Umar Namadi ya tarbi ‘yan adawa sama da dubu biyu da suka canza sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a yankin.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
