Labarai
Gwamna Namadi Ya Tsige Rabi’u Kaugama Daga Mukaminsa
Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya tsige Rabi’u Garba Kaugama daga mukaminsa na Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Majalisar Tarayya, nan take.
Wannan mataki an sanar da shi ne ga manema labarai cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim ya sanya wa hannu.
Sanarwar ta ce: “A sanadiyar wannan mataki, an dakatar da dukkan hakkoki da fa’idodi da suka shafi ofishinsa na Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Majalisar Tarayya.”
Bugu da ƙari, sanarwar ta umarci tsohon Mai Bai wa Gwamnan Shawara da ya mika dukkan kayan gwamnati da ke hannunsa ga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa nan take.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
