Connect with us

Ilimi

Jami’ar Ahmadu Bello Zaria Za Ta Horas Da ‘Yan Jarida Game Da Aikin Su

Published

on

Shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke zaria, Farfesa Adamu Ahmed ya ce jami’ar za ta hada kai da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya domin horar da mambobinta.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da mambobin kungiyar NUJ reshen Zaria suka kai masa ziyarar taya murna a ofishin sa da ke Zariya.

 

Shugaban jami’ar wanda ya bayyana su a matsayin abokan jami’ar, ya kuma ce babu wata gwamnati da za ta yi kasa a gwiwa wajen hada kai da ‘yan jarida.

 

Ya ce abubuwa masu kyau suna faruwa a jami’ar Ahmadu Bello ba tare da sanin jama’a ba.

 

Shugaban ya yabawa kungiyar bisa wannan karramawar, inda ya ce ya ji dadin wakilcin su a zariya.

 

Da yake jawabi tun da farko, Shugaban kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya reshen Zaria Malam Sagir Mohammed Awwal, wanda ya bayyana Farfesa Ahmed a matsayin mai kwazo, mai gaskiya da kirkire-kirkire, ya kuma taya ma’aikata da dalibai da daukacin tsofaffin daliban ABU murnar zaben Ahmed a matsayin shugaban kasa.

 

Sagir ya yabawa jami’ar bisa kyawun karatun ta, yana mai cewa gaggarumar gudumawar da take bayarwa wajen ci gaban Najeriya na da ban mamaki.

 

Ya ce an samu kyakyawar alaka tsakanin jami’ar da ‘yan jarida a zariya, kuma kungiyar na fatan samun kyakkyawar alaka.

 

Shugaban ya kuma ce mambobin kungiyar za su ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kwarewa wajen bunkasa harkokin ilimi a jami’ar.

 

Ya ce kungiyar na da mambobi 23 da suka gudanar da ayyuka a kananan hukumomi takwas na shiyyar Kaduna ta daya.

 

COV/HALIRU HAMZA

Labarai

Labarai8 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi9 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai9 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai11 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara