Labarai
Mataimakin Shugaban Tanzaniya Na Barazanar Yin Murabus Saboda Matsalar Karancin Ruwa
Mataimakin shugaban ƙasar Tanzaniya, Phillip Mpango ya yi barazanar sauka daga muƙaminsa saboda matsalar ƙarancin ruwan sha da aka daɗe ana fama da ita a lardin Mwanga da ke arewacin ƙasar.
Mista Mpango ya zargi ƴan kwangilar da ke kula da muhimmin aikin samar da ruwan sha a yankin na ɗaukan lokaci kafin kammala shi.
Shirin na sama da dala dubu 100 an soma shi ne kusan shekara 20 da ta gabata, a cewar Mista Mpango.
“Idan har aikin nan ba zai samar da ruwa ba ga mutanen yankin nan da watan Yuni, zan sauka.” Inji Mista Mpango.
“Ba zan sake zuwa nan na faɗa wa jama’a su ƙara hakuri ba, ruwa shi ne rayuwa,” ya ce.
A cewar jami’an gwamnati da suka yi wa Mista Mpango rakiya zuwa Mwanga a ranar Alhamis, an yi kashi 90 cikin 100 na aikin samar da ruwan.
-
Labarai5 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai4 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United