Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta kara zage damtse wajen farfado da mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi ta hanyar mayar da Cibiyar Gyaran Matan Gaya, wadda a da ya kasance gidan marayu, zuwa wurin gyaran tarbiya.

 

Kwamishiniyar harkokin mata, yara da masu bukata ta musamman, Hajiya Amina Abdullahi Sani, ta jagoranci wata babbar tawaga zuwa cibiyar da ke Gaya domin tantance bukatun gyare-gyare da kuma hada kai da ma’aikatu domin gudanar da aikin.

 

Tawagar ta hada da kwamishinan ayyuka Engr. Marwan Ahmad Badawi, tawagarsa ta fasaha, daraktoci, da mataimaka daga ma’aikatar harkokin mata.

 

A yayin ziyarar, kwamishinar ta bayyana wa takwararta na ma’aikatar ayyuka irin ayyukan da ake bukata domin inganta cibiyar, da suka hada da gyare-gyare da fadada gine-gine domin daukar da kuma gyaran tarbiyar mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi a cikin yanayi mai aminci da tallafi.

 

A nasa jawabin, kwamishinan ayyuka Eng. Marwan Badawi ya bayar da tabbacin cewa ma’aikatar ayyuka za ta hada kai da ma’aikatar harkokin mata domin bayar da tallafin fasaha da ababen more rayuwa.

 

“Za mu tabbatar da cewa wannan ginin ya cika ka’idojin da ake buƙata don tallafawa yadda ya kamata don farfado da matan mu da ke fama da shaye-shayen ƙwayoyi,”

 

Tawagar ta kuma kai ziyarar ban girma ga mai martaba Sarkin Gaya, inda suka sanar da shi shirin gwamnatin jihar na yin wannan hubbasa.

 

Sarkin ya bayyana goyon bayansa tare da yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya bayyana a matsayin jagoranci mai hangen nesa da tausayi.

 

Gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta ci gaba da jajircewa wajen baiwa masu karamin karfi tallafi tare da samar da yanayi mai kyau na farfadowa da sake dawo da mutanen da suke fama da shan miyagun kwayoyi musamman mata.

 

Rel/Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai6 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi6 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai6 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai8 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara