Ilimi
Mutane fiye da dubu 200 muka ba taimakon Lauya – Barista Aliyu
An bayyana bukatar sake nazarin tsarin shari’ar kasan nan muddun ana bukatar rage cinkoson da ake da shi a gidajen gyaran hali da ke fadin kasan nan
Gwamnan Jihar Plateau Caleb Muftwang ya bayyana haka lokacin da kungiyar bada tallafin aikin lauya ta kasa ta ziyarce shi a gidan gwamnati
Ita dai wannan kungiyar da ke bada agajin aikin lauya ga marasa karfj da ake tuhuma da aikata wani laifi ta zamo gatan marasa gata a kasan nan.
Don tabbatar da wannan kirarin da ake yiwa kungiyar, ta ziyarci dukkanin gidajen gyaran hali da ke kasan nan domin tabbatar da ta tallafawa wadanda ke tsare ba su da karfin daukar lauyan da zai Kare su.
Gwamnan jihar Plateau ya fadawa masu ziyarar cewa, saboda rashin adalci da daidaito ya sa ake samun aikata laifuka, don haka yace akwai bukatar yiwa tsarin shari’ar kasan nan gyaran fuska don maganin wannan matsala.
Gwamnan Wanda ya bayyana takaicin sa ganin yadda ake samun cinkoso a gidajen gyaran Hali da ke kasan Nan, yace ana shirin samarda Karin gidan gyaran Hali a Jos ta Gabas.
Tunda farko shugaban masu ziyarar kuma shugaban kungiyar Barista Aliyu Abubakar yace kungiyar su ta nada agajin lauya ga mutane fiye da dubu 200 daga shekara ta 2021 zuwa bara 2023, don yayi Kiran samun goyon baya ga kungiyar domin su ci gaba da aikin su.
Yace manufar kungiyar su, ita ce su samarda wata kasa da za a ce an Sami daidaita tsakanin dukkanin ‘yan kasa
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai6 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar