Labarai
Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe
An kaddamar da jam’iyyar African Democratic Party, ADC a Gombe mako guda bayan wasu jiga-jigan ‘yan adawa sun hada kai cikin jam’iyyar.
Shugaban jam’iyyar ADC a jihar Gombe kuma tsohon ministan sufuri Alh. Idris Abdullahi, ya ce makasudin shiga jam’iyyar shi ne ceto kasar nan daga kangin tattalin arziki da dora ta kan turbar ci gaba.
A cewarsa gamayyar jam’iyyun adawa sun zabi jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyya daya tilo da za ta samar da hanyar kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2027.
Sanata Idris Abdullahi ya jaddada kudirin kungiyar a Gombe na ci gaba da kasancewa da hadin kai domin cimma burin ta.
Shugaban jam’iyyar ADC na jihar Gombe Alh. Auwal Barde ya ce gamayyar ta nuna mafarin dabarun mayar da jam’iyyar a matsayin mai karfi a jihar da kuma yanayin siyasar kasar nan.
Ya ce jam’iyyar ta bude rajistar zama mambobinta domin karbar sabbin masu shiga tare da yin kira ga ‘yan siyasa da ba su gamsu da su daga wasu jam’iyyun siyasa da su shiga abin da ya bayyana a matsayin ingantacciyar hanyar siyasa.
Alh. Auwal Barde ya ba da tabbacin cewa jam’iyyar a shirye take kuma a shirye take ta ba da sabuwar alkiblar da ta shafi rikon amana, hada kai da kuma tafiyar da al’umma.
HUDU Shehu/Gombe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
