Labarai
Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
Mummunan lamari ya faru ne a lokacin da wata mota kirar bas ta kasuwanci da wata babbar mota ta yi taho-mu-gama da tare da daukar rayukan mutane 21 a hanyar Zariya zuwa Kano.
Hadarin ya afku ne a Kasuwar Dogo, Dakatsale, wanda ya hada da wata motar kasuwanci kirar Toyota Hiace da wata tirela ta DAF.
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta bayyana cewa, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar bas din ya saba ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa, lamarin da ya kai ga yin karo da babbar motar da ke zuwa.
Hatsarin ya yi sanadiyar mutuwar fasinjoji 21 nan take, wadanda suka hada da manya maza 19 da manya mata 2, yayin da wasu uku suka samu raunuka, kuma an kai musu daukin gaggawa.
Jami’an FRSC tare da sauran kungiyoyin bayar da agajin gaggawa sun isa wurin domin gudanar da aikin ceto tare da kwashe tarkacen motocin, wanda hakan ya baiwa ababen hawa damar ci gaba da amfani da hanyar.
Da yake tofa albarkacin bakinsa, Shugaban Rundunar FRSC, Marshal Shehu Mohammed, ya bayyana matukar alhininsa game da asarar rayuka da aka yi, ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa.
Ya kuma tabbatar da cewa, ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike domin gano cikakken al’amuran da suka faru a hatsarin.
“Wannan mummunan bala’i kuma wani abin tunawa ne mai raɗaɗi na mummunan sakamakon rashin biyayya ga dokokin hanya,” in ji shi.
“Tuƙi gangaci da wuce gona da iri sune manyan abubuwan da ke ba da gudummawa ga irin waɗannan bala’o’in da za a iya gujewa a kan hanyoyinmu.”
Rundunar ta Corps Marshal ta bukaci dukkan direbobi musamman masu sana’ar tuki da su bi ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa.
Ya kuma jaddada cewa za a kara kaimi wajen tabbatar da tsaro da wayar da kan jama’a domin hana ci gaba da asarar rayuka.
Hukumar ta FRSC ta yi kira ga masu amfani da hanyar da su kai rahoton hatsarita hanyar kiran lambar kyauta 122, ko kuma a tuntubi duk wata tawagar sintiri ta FRSC.
An ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a asibitin Nasarawa dake Kano, inda ake jiran tantancewa da kuma mikawa iyalansu.
Rel/Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
