Labarai
An Tabbatar Da Mutuwar Mutum Guda Tare Da Ceto Wata Mata Daga Rijiya
Wani mummunan lamari da ya faru a rijiya ya yi sanadin mutuwar wani mutum mai suna Salisu Musa dan shekara 50 a kauyen Gora da ke karamar hukumar Madobi a jihar Kano.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Alhaji Saminu Abdullahi ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Kano.
A cewar Saminu, wanda ya rasu yana fama da matsalar tabin hankali.
Ya bayyana cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, Salisu ya garzaya cikin daji, inda daga bisani ya fada cikin rijiya.
Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, duk da kiran da ya yi na neman agaji, babu wanda zai iya kubutar da shi har sai zuwan tawagar hukumar kashe gobara.
“An same shi a sume kuma daga baya aka tabbatar ya mutu”
“An mika gawarsa ga Sufeto Nuhu Daniel na rundunar ‘yan sandan Madobi don ci gaba da bincike”
Hakazalika hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta samu nasarar ceto wata mata mai suna Maryam Biya mai shekaru 37 da haihuwa wacce ita ma ta fada cikin rijiya da ke kan titin Faransa a karamar hukumar Fagge.
Ya ce, wani dan kasa, Joseph Pitter ya kai rahoton ga Babban dakin kula da kashe gobara.
Saminu ya jaddada cewa, da isar su, tawagar ceto ta fitar da Maryam daga rijiya da rai.
“Nan take aka garzaya da ita asibitin kwararru na Murtala Muhammad domin kula da lafiyarta”.
Ya kara da cewa daga baya an mika ta ga dan sanda Mu’azu Abdullahi na sashin ‘yan sanda na Sabon Gari.
Jami’in hulda da jama’a Saminu Yusif ya yabawa kokarin da kungiyoyin bayar da agajin gaggawa suka yi a wannan lamarin.
Ya kuma yi kira ga jama’a da su dauki matakan kariya, musamman a kusa da budadden rijiyoyi, domin hana afkuwar irin wannan mummunan lamari a nan gaba.
Khadija Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
