Connect with us

Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Rangwamen Kashi 50 Bisa 100 Na Takin Zamani

Published

on

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya raba tireloli uku uku na taki ga  Kananan Hukumomin jihar 44, tare da yin  rangwamen kashi hamsin bisa dari na kudaden takin ga manoma.

Kowacce tirela tana ɗauke da buhuna 600 na taki, wanda ya kai jimillar buhuna 79,200.

An kaddamar da bikin rabon takin ne a harabar kamfanin Al Yuma Fertilizer da ke karamar hukumar Madobi.

Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin noma wajen ci gaban jihar, inda ya ce: “Mun taru a nan ba kawai don raba buhunan taki ba, sai don tabbatar da kara inganta dogaro da kai, da habbaka tattalin arzikin.”

Gwamnan ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da gwamnati ta samu a fannin bunkasa noma, wadanda suka haɗa da faɗaɗa damar samar da filayen noma, da habbaka noman rani , da kuma bayar da sabbin ayyuka a kananan hukumomi 11.

Haka kuma, ya ambaci gina dam a Dansoshiya da ke karamar hukumar Kiru, domin tallafa wa aikin noma.

Ana sa ran yin rangwamen kashi hamsin bisa dari a kan takin  zai ƙara samar da abinci, habaka tattalin arziki, da wadatar abincin a jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa rabon taki a farkon damina ya zo a kan lokaci, wanda tabbas zai amfani manoma.

 

Abdullahi Jalaluddeen

Labarai

Labarai14 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara