Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Farfado Da Kasuwar Farm Centre Da Gobara Ta Lakume

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da wani kwamitin musamman domin bincike da kuma kula da abubuwan da suka biyo bayan gobarar da ta tashi a kasuwar wayoyin hannu da ke Farm Centre.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ne ya gudanar da bikin kaddamarwar a madadin Gwamnan Jihar.

An dora wa kwamitin nauyin bincikar musabbabin gobarar, sanin girman asarar da aka yi da kuma bayar da shawarwari masu amfani don kauce wa kara faruwar irin wannan iftila’i.

Da yake jawabi a wurin kaddamarwar, Alhaji Umar Farouk ya jaddada muhimmancin samar da tallafi bisa gaskiyada adalci, tare da gargadin gujewa siyasantar da shirin tallafawa waɗanda abin ya shafa.

Ya bukaci mutane, kungiyoyi da dukkan ‘yan Najeriya masu kishin al’umma da ke son bayar da taimako ga ‘yan kasuwar da gobarar ta shafa, da su tura tallafinsu ta hannun kwamitin ko kuma ta asusun ajiyar gwamnati na musamman da aka ware domin hakan:

Sunan Asusun: FARM CENTRE GSM MARKET FIRE INCIDENCE SUPPORT FUNDS ACCOUNT
Lambar Asusun: 1310076187
Banki: ZENITH BANK

An nadaKwamishinan Harkokin Musamman, Alhaji Nasiru Sule Garo a matsayin shugaban kwamitin, yayin da sauran mambobin kwamitin suka fito daga  ma’aikatun gwamnati, hukumomin tsaro, ƙungiyoyin ‘yan kasuwa da kuma masu zaman kansu daga sashen kasuwanci.

Gwamnatin Jihar Kano ta jaddada kudirinta na tallafawa waɗanda abin ya shafa da kuma sake gina kasuwar ta hanya mafi tsari.

Gwamnati  ta bukaci haɗin kai daga dukkan masu ruwa da tsaki domin cimma wannan manufa.

Rel/Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai16 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara