Connect with us

Labarai

Nasarorin Ma’aikatar Ayukka a Karkashin Shirin “Renewed Hope”

Published

on

 

Gwamnatin Tarayya ta fitar da cikakken rahoto na tsakiyar zangon mulki da ke bayyana muhimman nasarorin da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ta cimma daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025.

Rahoton, wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka ya gabatar, ya bayyana ci gaba mai ma’ana da aka samu a fannin gine-ginen ababen more rayuwa, musamman hanyoyi, karkashin shirin Renewed Hope Action Plan na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne ci gaba da aiwatar da shirin Highway Development and Management Initiative (HDMI), wanda ke amfani da tsarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu (PPP). Wannan tsarin ya ba da damar janyo hannun jari daga masu zaman kansu don gyara da gina sabbin manyan hanyoyi da ke haɗa manyan birane da cibiyoyin kasuwanci a faɗin ƙasar.

Ma’aikatar Ayyuka ta kuma canja fasaha wajen gina hanyoyi daga amfani da kwalta zuwa amfani da fasahar siminti (concrete technology), wacce aka sani da jurewa dogon lokaci da rage buƙatar gyare-gyare akai-akai.

Wannan sabon tsarin yana tabbatar da cewa hanyoyin da ake ginawa yanzu za su dawwama, za su kasance masu aminci, kuma su fi araha a nan gaba.

Rahoton ya kuma nuna yadda Ma’aikatar Ayyuka ta ke kirkirar hanyoyin samun kuɗi na musamman don aiwatar da manyan ayyuka.

Hanyoyin sun haɗa da fita kasuwa don neman jari, fitar da takardun lamuni na gine-ginen ababen more rayuwa, da kuma ƙara faɗaɗa haɗin gwiwa da masu zaman kansu.

Wannan ya taimaka wajen ɗora ma’aikatar kan tafarkin da zai kai ga ingantaccen sauyi duk da ƙalubalen tattalin arziki.

“Manufar Renewed Hope ba ƙalmar kamfen ba ce kawai — tsari ne mai rai da ake aiwatarwa a kowane yanki na Najeriya,” in ji rahoton. “Ma’aikatar Ayyuka na aiki ba dare ba rana don tabbatar da cewa al’umma sun ji daɗin wannan sauyi.”

Wasu daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa ko aka kammala sun haɗa da faɗaɗa titin Legas-Ibadan, aikin titin Abuja-Kano, da sauran hanyoyin haɗin jihohi da ke da mahimmanci ga ciniki, noma da haɗin kai na ƙasa.

Masana sun bayyana cewa waɗannan nasarori na nuni da gaskiya da nufin gyara ƙasa bisa tsari da tasiri. Da sauran shekaru biyu kafin ƙarshen wannan zangon mulki, ana sa ran za a ci gaba da jan ƙasa da sauri domin samar da ci gaba mai ɗorewa.

Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka (CRDCU) ya jaddada cewa bin diddigin aiki da nuna gaskiya a bainar jama’a su ne ginshiƙan tsarin mulki na Renewed Hope.

Yayin da Najeriya ke ci gaba da tafiya zuwa ga zamanancewar ababen more rayuwa, Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya na taka rawa mai muhimmanci wajen gina tubalin ci gaban ƙasa da haɗa al’umma da juna.

Bello Wakili

Labarai

Labarai3 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi3 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai4 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai5 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara