Labarai
Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
Rukunin ƙarshe na mahajjatan Jigawa 368 ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi zuwa Saudiyya don aikin hajjin shekarar 2025.
A wata hira da aka yi da shi a Radio Nigeria kafin tashinsu gaf da Asubahin Alhamis, Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya bayyana cewa rukunin ƙarshe na mahajjatan 368 sun fito ne daga ƙananan hukumomin Birnin Kudu, Buji, da Taura na jihar.

A cewarsa, wannan rukunin ƙarshe ya haɗa da Amirul Hajj na jihar, malamai masu wa’azi, wasu jami’an shiyyoyi da cibiyoyi, da kuma wasu jami’an hukumar.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana cewa, jihar ta kammala aikin tantance mahajjata cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

Ya yabawa Gwamnan jihar, Malam Umar Namadi, bisa goyon baya da haɗin kai da ya bayar ga hukumar.
Darakta Janar ɗin ya kuma yi kira ga sauran mahajjatan Najeriya da ba a ɗauka ba su ƙara haƙuri tare da ci gaba da karanta littattafan da aka basu lokacin bita da shirye-shiryen hajji a jiharsu.


A jawabin bankwana da ya gabatar a filin jirgin sama, Gwamna Umar Namadi ya shawarci mahajjatan da su yi addu’a don jiharsu da ƙasar baki ɗaya.
Namadi ya kuma ja hankalinsu da su bi dokokin da ƙasar Saudiyya ta shimfiɗa.


Wasu daga cikin mahajjatan da suka yi magana da Radio Nigeria kafin tafiyarsu sun gode wa Allah da ya basu damar zuwa kasa mai tsarki domin gudanar da aikin hajjin bana.
Sun yabawa shugabannin hukumar kula da jin daɗin mahajjata ta jihar Jigawa bisa tanadin abinci da abin sha da suka yi musu yayin da suke sansanin Alhazai da filin jirgi.


Mahajjatan sun bayyana jin daɗinsu da yadda aka tsara wa’azi tare da yabawa jami’an hukumar da yadda suka kula da su a sansanin Alhazai.
Radio Nigeria ya ruwaito cewa, jami’an hukumar shige da fice, kwastam, da NDLEA ne suka tantance mahajjatan tare da jakunkunansu masu nauyin kilo 8.
Usman Muhammad Zaria.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
