Connect with us

Labarai

Inter Milan Ta Je Ta Rike Barcelona A Champions League

Published

on

An tashi 3-3 tsakanin Barcelona da Inter Milan a wasan farko zagayen daf da karshe a Champions League da suka kara a Sifaniya ranar Laraba.

Inter Milan ce ta fara cin ƙwallo a daƙiƙa 30 da take leda ta hannun Marcus Thuram, ya zama na farko da ya ci ƙwallo a ƙanƙanin lokaci a daf da karshe a Champions League.

Daga nan Inter ta kara na biyu ta hannun Denzel Dumfries, wanda ya zama na farko daga Netherlands da ya ci ƙwallo ya kuma bayar aka zura a raga a daf da karshe a Champions League, tun bayan Wesley Sneijder a Inter a karawa da Barcelona.

Dumfries shi ne ya bai wa Thuram ƙwallon farko da Inter Milan ta zura a ragar Barcelona cikin ƙanƙanin lokaci.

Barcelona ta sa namijin ƙwazo a wasan, inda Lamine Yamal ya zare ɗaye a minti na 24 a wasan na hamayya.

Haka kuma ƙungiyar Sifaniya ta farke na biyun ta hannun Ferran Torres, bayan da Raphinha ya samar masa damar zura ƙwallon a cikin raga cikin sauƙi.

Ana tsaka da wasa Inter Milan ta kara na uku ta hannun Denzel Dumfries, sai dai minti biyu tsakani mai tsaron ragar Inter, Yann Sommer ya ci gida.

Kenan ta sanadin Raphinha, wanda shi ne ya buga tamaular – hakan ya sa ya yi kan-kan-kan da Cristiano Ronaldo, wanda yake da hannu a cin ƙwallo 20 a Champions League a 2013/14.

Raphinha, ɗan wasan tawagar Brazil, ya zura 12 a raga ya kuma yi sanadin cin tara a bana a babbar gasar tamaula ta nahiyar Turai.

Barcelona da Inter Milan sun fuskanci juna karo na 17 a babbar gasar zakarun Turai, inda ƙungiyar Sifaniya ta yi nasara takwas da canjaras shida aka doke ta wasa uku.

Barcelona ta yi wasa shida ba tare da an doke ta ba a gida a fafatawa da Inter Milan kenan a Champions League, wadda ta yi nasara biyar da canjaras ta biyu.

Kocin Inter Milan, Simone Inzaghi, ya ja ragamar wasa na 50 a Champions League, ya zama mai horarwa na bakwai daga Italiya da ya yi wannan ƙwazon.

Ranar Talata 6 ga watan Mayu, Inter Milan za ta karɓi bakuncin Barcelona a wasa na biyu zagayen daf da karshe a Champions League a Italiya.

Barcelona ta kawo wannan matakin bayan yin waje da Borussia Dortmund, ita kuwa Inter Milan ita ce ta fitar da Bayern Munich a zagayen kwata fainal.

Barcelona tana matakin farko a teburin La Liga da tazarar maki huɗu tsakani da Real Madrid ta biyu a kakar nan.

Ita kuwa Inter Milan tana ta biyun teburin Serie A da tazarar maki uku tsakani da Napoli mai jan ragamar babbar gasar tamaula ta Italiya.

Inter za ta karɓi bakuncin Verona a gasar Serie A ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ta kece raini da Barcelona a Italiya a Champions League ranar Talata.

Barcelona kuwa za ta je gidan Valladolid a gasar La Liga ranar Asabar 3 ga watan Mayu, sannan ranar Talata ta ziyarci Inter a wasa na biyu a Champions League.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara