Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Na Cigaba Da Ba Da Rarar Kudi Ga Alhazan 2023

Published

on

 

Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna tana kira ga dukkan alhazan da suka yi aikin hajji ta hannunta a shekarar 2023 da har yanzu ba a biya su rarar kudin da Hukumar Kula da aikin Hajji ta Kasa (NAHCON)ta dawo wa da Alhazan ba, cewa an rubuta masu takardar cek ta banki da za su je banki kai tsaye su karbi kudadensu.

 

 

Saboda haka, hukumar tana sanar da Alhazan da suka fito daga kananan hukumomin Kaduna ta Arewa da Kaduna ta Kudu da Kajuru, Igabi, Chikun, Birnin Gwari, su hallara a Cibiyar Musabakar Karatun Alkuráni a Kinkinau Tudun Wada Kaduna gobe Alhamis da Jibi Jumaáh 12 da 13 ga Maris don karbar wannan cek na kudadensu tun daga karfe 10 na safe.

 

 

Alhazan kananan hukumomin Ikara, Kubau, Kudan, Makarfi, Giwa, Soba, Sabon Gari da Zariya su hallara a hedkwatar Karamar hukumar Sabon Gari Ranar Asabar 14 ga Maris 2025 don raba masu cek na kudadensu na rara tun daga karfe 10 na safe.

 

 

Sauran alhazai da suka fito daga shiyya ta uku, wato Kudancin Jihar Kaduna, za su hadu a Cibiyar yi wa maniyyata Bita dake Kachiya ranar Lahadi 15 ga Maris don su karbi na su cek din.

 

 

Hukumar tana jawo hankalin alhazan cewa shaidar da take bukatar kowane alhaji ya gabatar it ace lambar kujera da kuma fasfo da suka yi aikin hajji a shekarar 2023.

 

Rel/Adamu Yusuf

Labarai

Labarai16 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara