Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Na Cigaba Da Ba Da Rarar Kudi Ga Alhazan 2023
Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna tana kira ga dukkan alhazan da suka yi aikin hajji ta hannunta a shekarar 2023 da har yanzu ba a biya su rarar kudin da Hukumar Kula da aikin Hajji ta Kasa (NAHCON)ta dawo wa da Alhazan ba, cewa an rubuta masu takardar cek ta banki da za su je banki kai tsaye su karbi kudadensu.
Saboda haka, hukumar tana sanar da Alhazan da suka fito daga kananan hukumomin Kaduna ta Arewa da Kaduna ta Kudu da Kajuru, Igabi, Chikun, Birnin Gwari, su hallara a Cibiyar Musabakar Karatun Alkuráni a Kinkinau Tudun Wada Kaduna gobe Alhamis da Jibi Jumaáh 12 da 13 ga Maris don karbar wannan cek na kudadensu tun daga karfe 10 na safe.
Alhazan kananan hukumomin Ikara, Kubau, Kudan, Makarfi, Giwa, Soba, Sabon Gari da Zariya su hallara a hedkwatar Karamar hukumar Sabon Gari Ranar Asabar 14 ga Maris 2025 don raba masu cek na kudadensu na rara tun daga karfe 10 na safe.
Sauran alhazai da suka fito daga shiyya ta uku, wato Kudancin Jihar Kaduna, za su hadu a Cibiyar yi wa maniyyata Bita dake Kachiya ranar Lahadi 15 ga Maris don su karbi na su cek din.
Hukumar tana jawo hankalin alhazan cewa shaidar da take bukatar kowane alhaji ya gabatar it ace lambar kujera da kuma fasfo da suka yi aikin hajji a shekarar 2023.
Rel/Adamu Yusuf
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai16 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
