Connect with us

Labarai

Wani Bawan Allah Ya Ɗauki Nauyin Ciyar Da Masu Azumi A Kano

Published

on

Wani mai taimakon al’umma a Kano ya fara gudanar da ayyukan jin kai ta hanyar bayar da abincin buda baki na azumin Ramadan kyauta ga marasa galihu a cibiyoyi goma a fadin jihar.

Ana raba Shinkafa da Kunun Tsamiya da taliyar yara, da dai sauran abinci, domin buda baki.

An kaddamar da wannan tallafin ne a daya daga cikin cibiyoyin ciyar da abinci da aka ware a garin Rimin-Gado ta hannun Barista Muhuyi Magaji.

Wadanda suka ci gajiyar tallafin sun fito ne daga sassa daban-daban na jihar, sun kuma nuna jin dadinsu da wannan tallafi.

Baya ga bayar da abincin buda bakin, wannan bawan Allah ya kuma raba kayan abinci da suka hada da shinkafa da taliyar yara, da tsabar kudi ga marasa galihu sama da 2,000 da marayu 150 don tallafa musu a cikin wannan wata mai alfarma.

Mai bada agajin wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa an yi hakan ne don neman yardar Allah, wanda ya umarci masu imani da su ciyar da marasa galihu musamman cikin watan Ramadan.

Wadanda suka ci gajiyar shirin da suka hada da Maijidda Iro da Sadiya Yusuf sun godewa masu taimakon bisa wannan karimcin da suka ce zai ci gaba da ciyar da su a cikin wannan watan na Ramadan.

Sun yi addu’ar Allah Ya mishi sakayya da mafificin alkhairi.

Abdullahi Jalaluddeen

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara