Ilimi
An Bukaci Musulmai Su Ware Dukiya Don Ayyukan Ci Gaban Al’umma – Cibiyar Al-Furqa
An bukaci Al ummar musulmi da su cire wani kaso daga cikin dukiyarsu wajen gudanar da wasu ayyukan cigaba da habbakasu don cigaban al umma.
Shugaban cibiyar ayyukan Alheri ta Al furqan dake Kano , Muhammad Abubakar ya bayyana bukatar hakan a lokacin wani taro na wayar da Kai kan wakafi da tasirinsa wajen cigaban al umma a da ya gudana a dakin taro na Jama atu Nasril Islam dake Jos, a jihar Plateau.
Dr Abubakar yace , Al ummomi na bukatan hazikan mutane da zasu zuba jari da za a dunga amfani da kudaden wajen tafiyar da ayyukan tallafawa al umma.
Ya bukaci Masu hannu da shuni da su dinga koyar da yayansu ayyukan taimakon al umma don dawwamar ayyukan Alheri bayan .
Hakalika, ya bayyana Karin samun yawaitan ayyukan Alheri da aka waresu na taimakon al umma da suka hada da makarantu , wurin koyon sana o e, da daukan nauyin gajiyayyu da sauransu da suke taimakawa wajen cigaban al umma.

Da yake nasa jawabin , Shugaban cibiyar bincike da tattara bayanai ta Mahanga research centre , ,Limamin massallacin sultan Bello, Dr Suleiman Muhammad Adam, yace ayyukan alheri da aka gudanar ta hanyar wakafi ,sun taimaka wajen kawo sauye sauye a rayuwan alumma da dama da suka hada da rayuwar marayu, marasa galihu ta hanyar daukan nauyin karatunsu da lafiyarsu.
Limamin na sultan bello ya bukaci kwararru kan harkar ilimin wakafi , da sukara wayar da kan Yan Kasarnan wajen fahimtar muhimmancin sa da gudunmawar da yake bayarwa wajen cigaban rayuwar al umma.
COV/ABUBAKAR ADAM
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai16 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
