Kasuwanci
Gwamna Sule ya rattaba hannu kan kasafin kudin shekarar 2025
Gwamna Abdullahi Sule na jihar nasarawa, ya rattaba hannu a kan kasafin kudi na naira biliyan 384.3.
Gwamnan yayin da yake gabatar da kasafin kudin a gidan gwamnati, ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin kasafin ya yi yadda ya kamata.
Gwamna Abdullahi Sule ya kuma tabbatar da aniyarsa na ganin an aiwatar da tanade-tanaden kasafin kudin yadda ya kamata tare da jaddada muhimmancin samar da ingantaccen kasafin kudi wanda zai dace da abin da ake tsammani a duniya.
Ya kuma yabawa kakakin majalisar da ‘yan majalisar jiha da kwamishinoni da jami’an ma’aikatar kudi ta jiha bisa yadda suka bayar da kyakkyawar gudunmawa kan kasafin kudin.
A nasa bangaren, kakakin majalisar dokokin jihar nasarawa, Mista Danladi Jatau ya ce kudurin ya bi dokokin da suka dace kafin ya zama doka.
Ya kuma yabawa ’yan majalisa na 7 a karkashin jagorancinsa bisa jajircewarsu wajen gudanar da ayyuka.
COV/Aliyu Muraki/Lafia. Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai14 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
